By Abbas Yakubu Yaura
Jami’ar Tarayya ta Albarkatun Man Fetur, Effurun, FUPRE, a ranar Alhamis, tace an dage atisayen tantancewa na Jarabawa Post UTME da aka shirya gudanarwa tun daga ranar Litinin 25 da kuma ranar Asabar 30 ga watan Oktoba na shekarar 2021.
Magatakardar jami’ar Mrs. Jane Omoyine a cikin wata sanarwa data fitar tace, “Wannan shi ne sanar da duk ‘yan takarar da suka zabi Jami’ar a matsayin Wadanda suka samu maki 150 da sama da haka a jarrabawar gama-gari ta (UTME) na wannan shekarar ta 2021 cewa za a gudanar da ita yanzu daga ranar Litinin, 22 zuwa Asabar 27 ga watan Nuwamba tsakanin karfe 8.00 na safe zuwa 5.00 na yamma kullum.
“Aikin yin rajista wanda ya fara a ranar Litinin 4 ga Oktoba 2021, zai ci gaba har zuwa ranar Laraba 17 ga watan Nuwamba.
Sannan ‘Yan takarar da suka cancanta su ne wadanda suka sami maki biyar (5) O’ a zaman Jarabawa daya ko biyu (ciki har darasin turanci dana Lissafi) ko kuma suna jiran sakamakon da za a fitar kafin kammala aikin daukar daliban.
“Nasarar shigar da sakamakon O’ Level akan jarawabawar JAMB ya zama tilas don shiga sannan an shawarci ‘yan takara da wuri su ziyarci kowace cibiyar CBT don sake saka cikakken sakamakon su na ‘matakin farko, idan ba tare da wadannan ba baza su dauki mutum ba.
Kazalika jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa “Daliban Masu neman takara za su biya Naira 2,000 a matsayin kudin tantancewa.
“Ka’idojin yin rijista shine
ya kamata ‘yan takara su Tabbatar da cewa sun cika fom ɗin akan layi a hankali, da kuma bin duk umarnin da suka dace. dayin watsi da umarni da gangan, kuskure (s) shigarda bayanai ba daidai ba zai haifar da rashin cancanta na dalibi.
Bayan kammala cika fam ɗin a kan layi kuma tabbatar da cewa duk bayanan da aka bayar daidai ne. Bayan haka, danna maɓallin aikawa wato ‘SUBMIT’ sannan kuma buga shafin tabbatar da yin rajista, a Lura da cewa ba za su iya gyara bayanan da aka bayar ba da zarar sun ƙaddamar. “