Ministan sufurin jiragen sama da ci gaban sararin samaniya, Mista Festus Keyamo ya ce kamfanin jiragen sama na Emirates zai koma aiki a Najeriya nan ba da jimawa ba.
Kakakin ma’aikatar, Odutayo Oluseyi ya bayyana haka a ranar Lahadi.
Karanta nanBa Na Kewar Fadar Shugaban Kasar Nijeriya–Buhari
A cewar Oluseyi, ministan ya gana da jami’an kamfanin Emirates Airline a 2023 a Dubai Airshow a UAE domin ci gaba da tattaunawa kan dawo da zirga-zirgar jiragen da kamfanin ya yi zuwa Najeriya wanda ya haifar da sakamako mai kyau saboda hukumar ta ba da tabbacin dawo da jirgin.
Sun kuma tabbatar da cewa gwamnatin Masarautar ta amince da jirgin saman Najeriya Air Peace Airline ya tashi kai tsaye zuwa filin jirgin sama na Dubai.
Ku tuna cewa kamfanin jiragen sama na Emirates ya dakatar da zirga-zirgar jiragensa zuwa Najeriya saboda rashin iya dawo da kudaden da suka makale a kasar.
Har ila yau, Oluseyi ya bayyana cewa, ministan ya gana da “hukumomin kamfanin jiragen sama, karkashin jagorancin shugaban kamfanin, Dana Hatcic, wani kamfani da ya nuna sha’awar kafa cibiyar MRO a Najeriya.
Mahukuntan sun tattauna da mai girma Ministan inda aka gayyace su zuwa Najeriya domin ci gaba da bibiyar tsare-tsaren kasuwancinsu.
A wani labarin kumaZan Hukunta Jami’an Gwamnatina Da Suka Ki Zaben Ododo-Yahaya Bello
Ministan ya bayyana yiwuwar kashi na farko na Nigerian Airshow a wani lokaci a watan Nuwamba 2024, ta yadda za ta zama kasa ta farko a Afirka da ta shirya irin wannan taron. Wasu daga cikin masu baje kolin a Dubai Airshow sun yi alkawarin kasancewa a kashin farko na Airshow na Najeriya.
An kammala bikin Airshow na Dubai Airshow wanda ya fara a ranar 13 ga Nuwamba a ranar 17 ga Nuwamba, 2023 ya jawo ɗimbin mahalarta daga ko’ina cikin duniya, gami da manyan ƙwararrun masana’antar jiragen sama da sararin samaniya.