Gwamnatin jihar Kano ta yi kakkausan gargadin cewa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen soke lasisin gudanar da harkokin kasuwanci na manyan ‘yan kasuwa ko kuma daukar mataki kan duk wanda ya ki karban tsohuwar takardar naira a matsayin hanyar ciniki.
Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, wanda ya yi wannan gargadin a wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Malam Muhammad Garba ya fitar, ya ce har yanzu kudaden na naira na nan a matsayin doka.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ina Aiki Tare da Peter Obi – Gwamnan G5
Ya ce kotun koli ta jaddada hukumcin wucin gadi da ta yi kan batun tsofaffin takardun kudin Naira da za a ci gaba da amfani da su hannu da hannu da sabbi har sai an kammala shari’a.
JARIDAR DIMOKURADIYYA ta rawaito cewa Gwamnan ya yi nuni da wasu ‘yan kasuwa kamar manyan kantuna, bankuna, gidajen cin abinci, otal-otal, ‘yan kasuwa a kasuwanni, gidajen mai, wuraren ajiye motoci, da dai sauransu, suna da dabi’ar kin karbar tsohon kudin naira a hada-hadar kasuwanci su inda yace ba zasu lamuci hakan ba.
Ganduje ya kara da cewa rashin amincewa da wasu masu son kai na kara dagula al’amura da dama da rashin samun sabbin takardun kudin Naira.
Sanarwar ta kara da cewa, “Ayyukan kasuwanci da na tattalin arziki sun yi matukar tasiri wajen sake fasalin kudin Naira, kuma abin takaici wasu masu son kai ne suke kashe kudi domin su kara jawo wa jama’a wahalhalu ta hanyar kin karbar tsoffin takardun naira a yayin hada-hadar kasuwanci.
Ya ce jama’a sun sha wahalhalun da ba a zayyana ba, don haka gwamnatin jihar ba za ta nade hannunta ba, ta bar wasu masu son kai a cikin mu su dagula lamarin.
Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da gudanar da sana’o’insu na halal tare da kai rahoton duk wanda ya ki karban tsohuwar takardar naira zuwa wuraren da suka dace.
A wani labarin kuma, Shugabar YouTube Susan Wojcicki Ta Yi Murabus Daga Mukaminta
Babbar jami’ar YouTube, Susan Wojcicki, ta yi murabus daga mukaminta bayan ta shafe shekaru tara tana jan rakamar sa.
Wojcicki, wanda ta shiga isGoogle a matsayin ma’aikaciya ta 16 a shekarar 1999, ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis.