An Yanke wa Wani Mutum Mai shekara 52 Nkereuwem Etim Emah, hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda ya kashe matarsa mai ciki.
Emah, dan asalin Mbiabam, karamar hukumar Ibiono Ibom, ta jihar Akwa Ibom, ya zargi matar sa mai juna biyu da rashin imani.
Wanda ake zargin, mai ‘ya’ya biyar ne, an ce ya yanka matarsa har lahira bayan wata arangama da suka yi a kan uban jaririn da ta haifa.
Da yake magana a matsayin mai gabatar da kara a wata babbar kotun Uyo, Christian Sylvanus Etim, dan marigayin mai shekaru 10, ya bayyana yadda mahaifinsa ya kashe mahaifiyarsa.
“A ranar 12/2/2018, mahaifina (mai kanikanci ne a hukumar ruwa), ya yi amfani da ashana da dare lokacin da mahaifiyata ke barci, ya yanka mahaifiyata. Mahaifiyata ta rasu,” inji shi.
Da yake tabbatar da wannan magana, wanda ake zargin wanda ya shaida wa ‘yan sanda bayan kama shi, ya ce “A ranar 12 ga Fabrairu, 2018, da misalin karfe 4:30 na safe, na kira matata na tambaye ta yadda ta samu cikin da kuma wanda ke da alhakin hakan.
“Ta ki amsa min sai na ji haushi. Na dauki katon wuka na yanke hannunta na dama. Ta matsa don gudu, na sake yanke mata wuya ta fadi.
“Mutanen da ke kusa da gidanmu sun gaya mini cewa wani Michael Udoh yana kwana da ita a duk lokacin da na bar gidan don aiki,” in ji shi.
A cikin hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Bassey Nkanang ya bayyana wannan aika-aika a matsayin “abin kunya, da ba za a iya bayyanawa ba, kuma mara uzuri ga gidan aure.”
“Yanayin makamin da wanda ake tuhuma ya yi amfani da shi wajen huce haushinsa a kan wanda aka kashe, hakan ya nuna karara cewa wanda ake zargin ya yi niyyar kashe marigayin a fili.
“An sami wanda ake tuhuma da laifin kisan kai kuma an yanke masa hukunci.
“Wanda ake tuhumar, Nkereuwem Etim Emah, an yanke masa hukuncin kisa ne bisa bin sashe na 339(2) na dokar laifuka, Cap 39, na dokokin jihar Akwa Ibom.
“Hukuncin da kotu ta yanke maka, Nkereuwem Etim Emah, shine a rataye ka har sai ka mutu kuma Ubangiji ya ji tausayinka.” Kotun ta yanke hukuncin.
Bayan yanke hukuncin, wanda aka yankewa laifin ya roki kotun da ta yi masa adalci da rahama kuma ta sake ba shi damar komawa gida ya dauki ‘ya’yansa biyar.