Kungiyar likitocin Nijeriya, NARD ta sanar da janye yajin aikin da membobinta suka tsunduma.
A gobe Litinin 22 ga watan Yuni ne za su dawo daga yajin aikin, hakan ya faru ne bayan ganawar uwar kungiyar ta yi da wakilan gwamnatin shugaban kasa Buhari kan bukatun da suka tilasta musu tafiya yajin aikin gargadin.
Cikin wata sanarwar bayan taro da kungiyar ta raba mai dauke da sa hannun shugabanta na kasa Dr Aliyu Sokomba, ta ce sun dauki matakin janye yajin aikin ne don baiwa gwamnatocin jihohi da tarayyar damar cika alkawuran da suka dauka.
A cewar sanarwar tun farko shugaban majalisar wakilan kasar Femi Gbajabiamila da sakataren gwamnati Boss Mustapha da kuma shugaban kungiyar gwamnonin kasar Kayode Fayemi ne suka shiga tsakanin gabanin amincewa da matakin janye yajin aikin.