Mukaddashin shugabar hukumar kula da ayyukan ‘yan sanda, mai shari’a Clara Ogunbiyi mai ritaya, ta fara aiki a hukumance sa’o’i 24 bayan Musiliu Smith ya yi murabus.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito musamman yadda aka tilastawa Smith yin murabus bisa wasu batutuwa da suka shafi hukumar.
Da take jawabi jim kadan bayan ta kama aiki, Ogunbiyi, wadda har sai da aka nada ta a matsayin kwamishina 1 a hukumar kuma na gaba ga tsohon shugaban, ta yi alkawarin gudanar da mulki yadda ya kamata.
Ta kuma yi alkawarin tabbatar da cewa hukumomin da ke karkashinta za su yi duk mai yiwuwa don baiwa Ma’aikatan, Hukumar da za su yi alfahari da ita.
Tsohuwar mai shari’a ta kotun kolin ta nuna godiya ga abokan aikinta bisa amincewar da aka yi mata, inda ta ce hukumar ta cancanci kyakkyawan sakamako.
“Za mu yi iya kokarinmu da yardar Allah kuma na yi imani za mu yi aiki mai kyau. Wannan gudamarwar a yanzu za ta gudanar da harkokin gwamnati tare da tabbatar da an warware dukkan batutuwan da ke faruwa a kasa,” in ji ta.
A halin da ake ciki, Majalisar Hadin Gwiwar Hukumar ta dakatar da yajin aikin da ta ke yi na tsawon lokaci, tare da yin nuni da cewa tana son baiwa sabbin shugabannin hukumar damar duba bukatun ta.
Shugaban kungiyar ta hadin gwiwa, PSC reshen, Adoyi Adoyi, a wata tattaunawa da ya yi da wakilinmu, ya bayyana cewa, nan da nan bayan ficewar tsohon shugaban, shugabannin kungiyar sun yanke shawarar kiran majalisar domin tsara hanyar da za a bi.
“Mu ba Allah ba ne amma muna fatan cewa abubuwa za su canja da kyau tare da wannan sabon ci gaba. Mun yanke shawara a taronmu cewa a dakatar da yajin aikin,” inji shi.
Binciken da Daily trust ta yi ya nuna cewa an kaddamar da shugabancin Hukumar ne a ranar 25 ga watan Yuli, 2018 kuma ana sa ran za ta fita a ranar 24 ga watan Yuli 2023 kamar yadda doka ta tanada.
Sauran kwamishinonin da aka nada a 2018 tare da Smith da Ogunbiyi sun hada da: Lawal Bawa AIG Rt, CON (Kwamishina mai cikakken iko, Arewa maso Yamma); Mohammed Najatu (Mamba, Arewa maso Yamma); Braimoh Austin (Mamba, Kudu maso Kudu); Barista Rommy Mom (Member, Arewa ta tsakiya) da Dr Nkemka Jombo-Ofo (Member, Kudu maso Gabas)
A wani labarin kuma: Ƙaryane Bama Ɗaukar Ma’aikata — Inji Jami’ar NOUN
Jami’ar NOUN ta ce ba ta daukar ma’aikata ba tare da bin matakan da suka dace na daukar ma’aikata.
Daraktan yada labarai da wayar da kan jama’a na cibiyar Ibrahim Sheme ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar yayin da yake mayar da martani kan wasu labaran karya na daukar ma’aikata a yanar gizo.