- Bayan kama wani dalibin FUTA ɗan aji 5 wanda ya rasu kwanaki kadan da fara jarrabawar ta
- Marigayin, Akeredolu Clinton Ayomide, ya rasa ransa ne sakamakon rashin sanin makamar aiki da cibiyar lafiya ta jami’ar ta yi.
- Rasa matashin dalibin dan Najeriya ya sa abokan karatunsa gudanar da zanga-zanga a ciki da wajen jami’ar, lamarin da ya dakile zirga-zirga
Ɗaliban jami’ar Fasaha ta tarayya dake Akure (FUTA) a ranar Juma’a, 25 ga watan Agusta, sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewa da mutuwar wani dalibi ɗan aji 5 na jami’ar, Akeredolu ‘Clinton’ Ayomide.
Ayomide ya faɗi ya mutu a yammacin ranar Alhamis, 24 ga watan Agusta.
Ɗalibai sun zargi asibitin makaranta da mutuwar abokin karatunsu
Daliban sun tare hanyar Akure/Ilesha mai cinkoson jama’a da ababan hawa na tsawon sa’o’i da dama, lamarin da ya sa matafiya suka makale, kamar yadda majiyarmu ta rawaito.
KARANTA WANNAN LABARIN:
Sun yi zargin cewa cibiyar kula da lafiya na makarantar ba ta da kayan aikin ceton rayuka, wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwar Ayomide, in ji rahoton The Punch.
Majiyarmu ta fahimci cewa a ranar Laraba 30 ga watan Agusta, 2023 za a fara jarrabawar zangon farko na FUTA na shekarar 2022/2023.
Daya daga cikin daliban, wanda ya zanta da manema labarai ya bayyana cewa: “Mun garzaya da shi asibitin da misalin karfe 8:30 na dare. Lokacin da muka isa wurin, an sami katsewar wutar lantarki, kuma duk iskar oxygen da aka kafa, CPR da alluran da suka yi masa, hasken bai dawo ba. “Dole ne mu yi amfani da fitilun mu. Wannan yana da wuya a yarda cewa babu wutar lantarki a asibitin.”
Sai dai a martanin da Jami’ar ta yi game da mutuwar dalibin, Daraktan Sadarwa na, Adegbenro Adebanjo, ya yi kira da a kwantar da hankula tare da yin kira ga daliban da suka yi zanga-zangar. A wani bangare na bayanin ya karanta kamar haka:
“Daga rahoton da aka tattara tare, Ayomide Akeredolu ya fadi a cikin dakin kwanan dalibai kuma duk kokarin da likitoci suka yi don dawo masa da lafiyar jiki sa amma abin ya ci tura har ma a Cibiyar Kiwon Lafiya ta kasa tare da bayanan likitocin cewa an kawo shi a mace.”