Akalla manoma 27 ne ’yan bindiga suka sace a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari da ke Jihar Kaduna.
Lamarin ya faru ne yayin da manoman ke kan hanyarsu ta zuwa gonakinsu da misalin karfe 9:30 na safe a yankin Tsaunin Kunei da ke Karamar Hukumar Chikun ta jihar, a ranar Lahadi.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mutum tara daga cikin manoman mazauna kauyukan Udawa, Marinai da Damari na Jihar Kaduna ne, ragowar 18 kuma sun fito ne daga kauyukan Kusheka, Mashekari, Lukwape da Shiroro na Jihar Neja.
Shugaban yankin Udawa, Mohammed Umaru ya tabbatar da faruwar lamarin ga jami’an tsaro.
A cewarsa, har yanzu ’yan bindigar ba su tuntubi iyalan mutane da suka sace ba kan yadda za a yi kafin sakin nasu.
Ya bayyana cewa mazauna kauyukan da ke kan hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari suna cikin firgici duk lokacin da za su je gonakinsu saboda tsoron za a iya sace su.
A wani labarin Kuma na daban.
Aposto Johnson Suleman na cocin Omega Fire Ministries ya ce ’yan Najeriya ba zasu aminta da ’yan kabilar Igbo ba saboda ba sa tallafa wa kansu.
Malamin, yayin da yake wa’azi a cocinsa, ya ce ‘yan kabilar Igbo suna ruguza kansu a duk wata dama da aka ba su.
Da yake tsokaci kan yadda ‘yan kabilar Igbo suka fafata da juna, Suleman ya ce wani dan kabilar Igbo Chuba Okadigbo ne ya tsige shugaban majalisar dattawa, Evan Enwerem.
A cewarsa, an kuma maye gurbin Okadigbo da Anyim Pius Anyim.
Limamin ya bayyana cewa wanda zai iya sayar da dan uwansa ba zai amince da kowa ba.
‘’Wani daga Kudu, wani daga Gabas. Kuna cin amanar mutanen ku. Ku kalli wannan tada zaune tsaye na kungiyar Biafra. Su waye suka fi kai hari kan jama’a ‘yan kungiyar Biafra ne, Igbo marasa kunya ne.
“Ina goyon bayan raba Najeriya, A’a! Ina goyon bayan rabuwar Najeriya, A’a na yarda mu kasance tare? Ee. Amma ko da ba ka yarda da mutumin da yake ɗan’uwanka ba, ya kamata ka faɗa a fili idan kai ba wawa ba ne? Ba za ku iya faɗa a cikin mutanenku ba?”a cewarsa.
Ya kuma yi zargin cewa idan dan kabilar Ibo ya dauki wani yaro dan kabilar Igbo aiki a shagonsa, yaron zai lalata shi.
“Zai kwashe duk kudin mutumin, zai sayi fili. Ba zai jira a daidaita ba.
“Matsalar Igbo ita ce Igbo. Na sake maimaitawa, idan ka sayar da dan uwanka, ko masu siye ba za su amince da kai ba,” inji shi.