Dan takarar gwamnan jihar Kaduna Sanata Uba Sani ya bukaci al’umma da su gyara halayensu yayin cudanya da sauran mutane sai an zama na gari.
Sanata Uba Sani ya yi wannan magana ne ya yin da halarci taron da kungiyar lauyoyi Musulmi ta kasa MULAN reshen jihar Kaduna ta shirya, wanda shi ne Bako na musamman.
KARANTA KUMA Kungiyar Yan Jaridu Ta Karrama Sanata Uba Sani Da Lambar Yabo
Taron mai taken “Gudunmawar Addinin Musulinci da tsammanin da ake wa musulmi a al’amuran Dimokuradiyya”, an gudanar da taron a karshen makon jiya.
Sani ya ce “Dole kowa ya sauya a cikin Al’ummarmu, dole ne mu shiga cikin shirin zabe.
Ya kuma bukaci mahalarta taron da su kasance masu kula da kyawawan dabi’u da wayar da kan jama’a kan muhimmancin mutunta hakkin wasu.
Jaridar DIMOKURADIYYA ta rawaito taron ya sami halartar muhimman malamai don tsara hanyoyin da za a bi wajen nuna rawar da musulmi za su taka don tabbatar da kyawawan dibi’u da tabbatar da adalci a tsarin Dimokuradiyya.
Wasu hotuna na wajen taron
A Wani Labarin Kuma Shehu Sani Ya Mayar Da Martani Ga Kalaman Atiku Kan Amfani Da Cibiyoyin Kiwon Lafiya Na Kasashen Waje
Tsohon dan majalisar dokokin Najeriya, Sanata Shehu Sani, ya mayar da martani kan ikirarin Atiku Abubakar na cewa zai yi amfani da cibiyoyin kiwon lafiya na kasashen waje idan aka zabe shi a 2023.
Atiku, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, ya bayyana a jerin taron gidan talabijin na Arise, a ranar Lahadi, cewa mai yiwuwa ba zai dogara kacokan ga asibitocin Najeriya don kula da lafiyar sa ba idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaben shugaban kasa mai zuwa.