Sanata mai wakiltar mazabar Edo ta Arewa, Adams Oshiomhole, a ranar Litinin, ya ce shugaban kasa Bola Tinubu ya gaji mummunan yanayin tattalin arziki daga gwamnatin da ta shude ne, Punch ta rahoto.
Tsohon shugaban jam’iyyar APC ya kuma bayyana cewa wasu daga cikin hukunce-hukuncen da gwamnatin shugaba Tinubu ta dauka su ne matakin farko na sake fasalin tattalin arziki.
KARANTA WANNAN: Majalisar Dokokin Yobe Ta Fitar da Jerin Sunayen Kwamishinoni 20 da Zata Tantance
Da yake magana yayin wata tattaunawa da manema labarai jim kadan bayan ganawarsa da mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima, bayan da suka sanya labule a fadar shugaban kasa ta Villa dake Abuja ranar Talata, Oshiomole ya ce.
“Gwamnati ta gaji mummunan yanayin tattalin arziki, kowa ya sani. Gwamnati ta gaji tattalin arziki wanda jimillar kudaden shiga na kasa ya yi kasa a gwiwa wajen biyan bashi. Kashe kashi 96 cikin 100; wato duk Naira dari da Najeriya ta samu, kwabo casa’in da shida ne za a biya bashi”.
A halin da ake ciki, tsohon gwamnan Edo ya bayyana kwarin gwiwar cewa za a gaggauta warware matsalolin da suka taso daga cire tallafin man fetur tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyoyin kwadago.
A cewarsa, Tinubu ya fahimci irin tasirin da janye tallafin man fetur ke yi ga ‘yan Najeriya, kuma ya kuduri aniyar daukar matakin da ya dace domin dakile hakan.
Ya ce, “Shugaban ya fahimci cewa tasirin janyewar ya riga ya zo nan, mutane sun riga sun shiga wani yanayi na rashin jin daɗi don haka dole ne a gaggauta magance shi.
“Yanzu mafita nan da nan ita ce abin da muka tattauna kuma kasancewar muna ganawa a ranar Talata ya sake nuna cewa a fili, mun fahimci cewa wannan ba yana cikin abubuwan da kuke son siyan lokaci ba saboda yana da mummunan tasiri.
“Amma muna da mafita game da shi saboda za ku yi tanadi, don haka ku ɗauki wannan ajiyar ko ma aro ne.
“Don haka, duk abin da yake, za ku iya amfani da wasu kudaden shiga da inganta albashi don rage tsadar rayuwa, ina ganin ya dace, ina ganin abu ne mai yiwuwa, ba wani abu ba ne da kuke son kashe watanni biyu zuwa uku kuna tattaunawa.” Yace.
A wani labarin kuma, EPL: Keane Ya Yi Hasashen Yadda Man City da Man Utd Zasu Kare A Kakar Wasan Bana
Tsohon kyaftin din Manchester United, Roy Keane, ya ce tsohuwar kungiyarsa za ta kare a matsayi na hudu a gasar Premier ta bana.
Keane, ba ya tsammanin Red Devils za ta kawar da abokiyar hamayyarta Manchester City, wadda ya yi hasashen za ta sake lashe gasar.