Tinubu ya gaji mummunan tattalin arziki daga Buhari – Fadar shugaban kasa ga Atiku
Fadar shugaban kasa ta zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023, Atiku Abubakar da munafunci kan sukar da yake yiwa shugaban kasa Bola Tinubu.
Bayo Onanuga, mai ba Tinubu shawara na musamman kan yada labarai da dabaru, ya roki Atiku ya fadi gaskiya kuma ya yarda cewa shugaban kasa ya gaji raunin tattalin arziki daga magabacinsa, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.
KARANTA WANNAN LABARIN:Tinubu ya ceci Najeriya daga tabarbarewar tattalin arziki – Fadar Shugaban kasa
Onanuga ya ce sabanin sukar Atiku, Tinubu na kokarin gyara tattalin arzikin Najeriya.
Onanuga ya zargi Atiku da cewa ba shi da tushe a zahiri, ya ce alkaluma na baya-bayan nan sun nuna cewa har yanzu ’yan Najeriya na samun mafi karancin tsadar rayuwa a Afirka.
A wata sanarwa da Onanuga ya sanya wa hannu, ta ce: “Yan Najeriya cikin sauki za su iya gane munafuncin Atiku, wanda ke zargin Shugaba Tinubu da rashin mayar da martani ga kalubalen da al’ummar kasar ke fuskanta da kuma haddasa radadi da yanke kauna, bai bayar da wani zabin da ya fi dacewa da shi ba a takararsa na Shugaban kasa, daban da ajandar sake fasalin tattalin arzikin da shugaba Tinubu ke aiwatarwa.
“Ya kamata Atiku ya yi gaskiya don ya yarda cewa Shugaba Tinubu ya gaji raunin tattalin arziki, wanda bisa ga dukkan alamu da kuma tabbatar da dorewar kasarmu na bukatar gyara gaba daya.
“Ikrarin Atiku na cewa kamfanoni masu zaman kansu suna raguwa kuma kamfanoni na kasa da kasa suna barin kamfanoninmu a cikin ‘kumburi’ ba a kan gaskiya ba.”
Ya tuna cewa shugaban ya cire tallafin ne bayan hawansa mulki tare da bayyana shirin daidaita farashin canji.
Onanuga ya kalubalanci Atiku da ya gaya wa ‘yan Najeriya abin da zai yi daban-daban dangane da tattalin arziki idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa maimakon ya rika yin suka.
A wani labarin kuma:NYSC ta dakatar da tura masu yiwa ƙasa hidima zuwa ‘jahohin da ba su da tsaro
Hukumar masu yi wa kasa hidima ta kasa NYSC, ta ce shirin ya dakatar da tura masu yi wa kasa hidima zuwa jihohin da ake ganin ba su da tsaro sakamakon tabarbarewar tsaro a kasar.
Ministar Matasa, Jamila Ibrahim, ta bayyana hakan a wata hira da ta yi da gidan Talabijin na Channels.