Nasir El-Rufa’i, tsohon gwamnan jihar Kaduna, ya ce ya kamata a karfafa al’adun mulkin da ya shafi ‘yan kasa a kasar
The Cable ta ruwaito cewa El-Rufai yayi wannan magana ne a ranar Lahadin da ta gabata a wajen kaddamar da wani littafin tarihin rayuwa da ritaya na Ishaq Akintola, farfesa a jami’ar jihar Legas (LASU)
Kwanan nan Akintola ya yi ritaya daga jami’a bayan ya cika shekaru 70 da haihuwa.
El-Rufai, wanda shine babban mai jawabi kuma mai bayar da lambar yabo a wajen taron, ya ce gwamnatin Tinubu na kan turbar da ta dace don ganin Najeriya ta yi aiki da shawarar da ya yanke ya zuwa yanzu
KARANTA NANBa Rashin Daukar Kiran Tinubu Yasa Muka Kama Yari Ba-DSS
Tsohon gwamnan ya bayyana cewa, kyakkyawan tsarin da gwamnatin ta fara ya kunyata wadanda ba su ga wani alheri a tikitin addini daya ba
Hanyar da gwamnati mai ci ke bi wajen canza al’amura domin amfanin al’ummar Najeriya cikin kankanin lokaci ya nuna cewa shugabanci ya dogara ne akan kwarewa ba bisa cancanta ba
Dole ne mu rage ba da muhimmanci ga addini da kabilanci domin mu gina al’ummar da ba za a nuna wariya ga kabilanci ko addini ko ra’ayin siyasa ba
A matsayinmu na manyan kungiyoyin addini guda biyu a kasar nan, idan muka samu kanmu a cikin jama’a, ya kamata
Mu tabbatar da cewa mun yi aiki da ka’idojin shugabanci kamar yadda aka tsara a cikin addinan Kirista da na Musulunci
Dukan addinan biyu sun amince da al’adar jagoranci nagari, amma wasu mutane suna yin abin da ya saba da nassosi
El-Rufai ya ce zabin shugabanci bisa turbar addini ya saka Jahar Kaduna cikin mawuyacin hali a shekarun baya
Amma da yazo sai ya canza hakan aka dawo zabe kan turbar kwarewa a aiki ba wai a zabe ka don kana Kirista ko Musulmi ba
A WANI LABARIN KUMA
Sanatar Abuja Ta Ziyarci Wuraren Da Ambaliya Tayi Barna Kuma Ta Bada Tabbacin Gyarawa
Sanata mai wakiltar Abuja Sen Ireti Kingibe ta ziyarci wuraren da ambaliyar ruwa ta yima barna a wasu unguwanni na Abuja inda ta nemi da su kwantar da hankalinsu gwamnati na iyakar kokarin ta na gyara wuraren da suka lalace