Shugaban kasa, Asiwaju Bola Tinubu, ya aikewa majalisar wakilai wasika a hukumance yana rokon a tabbatar da sabbin shugabannin hafsoshin tsaro da aka nada.
Bukatar na kunshe ne a cikin wata wasika da kakakin majalisar Tajudeen Abbas ya karanta a zauren majalisar yayin zamanta na ranar Alhamis.
KARANTA WANNAN: Majalisar Dokokin Jigawa Ta Tantance Kwamishinonin da Gwamna Ya Aike Mata
A cikin wata wasika da ya aike wa shugaban majalisar kuma aka karanta a zauren majalisar, shugaban ya bukaci ‘yan majalisar da su yi la’akari da gaggawar tabbatar da hafsoshin tsaro da kuma babban hafsan tsaro kamar yadda wasu dokoki suka tanada.
Hafsoshin sojojin da za a tabbatar sun hada da Manjo Janar C.G Musa, babban hafsan hafsoshin tsaro; Manjo T. A Lagbaja, babban hafsan soji; Rear Admiral E. A Ogalla babban hafsan sojin ruwa da kuma AVM H.B Abubakar shugaban hafsan sojin sama.
Shugaban a cikin wasikar ya ce bukatar ta yi daidai da tanadin sashe na 18 (1) na dokar rundunar sojin kasa, Cap A20 na Tarayyar Najeriya shekarar 2004.
Jaridar PUNCH ta rawaito cewa shugaban kasar ya nada shugabannin hafsoshin tsaro a lokacin da majalisar dokokin kasar ke hutu.
Wasikar ta karanta a wani bangare cewa, “Bisa tanadin sashe na 18(1) na dokar rundunar soji. CAP A20 ta Tarayyar Najeriya shekarar 2004, na yi farin cikin gabatar da wannan wasika, don Majalisar Dattawa ta tabbatar da wadannan mutane hudu da aka zayyana a kasa a matsayin Hafsan Hafsoshin Tsaro da Hafsoshin Sojin Tarayyar Najeriya.
“An gayyaci Majalisar Wakilai ta lura da yanayin tsaron da kasarmu ke ciki a halin yanzu wanda ke bukatar hadin kan majalisun dokoki da na zartaswa don tabbatar da kasa mai cikakken tsaro.”
Wasikar ta kara da cewa: “Manjo Janar C.G Musa, babban hafsan tsaro; Manjo. T. A Lagbaja, babban hafsan soji; Rear Admiral E. A Ogalla babban hafsan sojin ruwa da kuma AVM H.B Abubakar shugaban hafsan sojin sama.
“Wannan ya sanar da sake duba Tsarin Gine-ginen Tsaron mu da nadin sabbin shugabanni don yin aiki tare da juna don cimma kyakkyawan aikin da ake tsammani daga Sojoji.
“Yayin da nake fatan bukatar ta samu cikakken nazari don majalisar wakilai ta tabbatar, don Allah a yarda, R.t Hon. Shugaban majalisa, tabbacin mafi girma na.”
A wani labarin kuma, Najeriya Tana Da Aminci Ga Masu Zuba Jari Na Kasashen Waje – Akpabio
Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya baiwa masu zuba jari na kasashen waje tabbacin tsaron jarin da suke zubawa a Najeriya.
Ya nanata cewa kudurin gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Bola Tinubu zai samar da kyakkyawan yanayin kasuwanci ga masu zuba jari na kasashen waje a kasar nan.