Tsofaffin Naira har yanzu suna aiki a jihar Jigawa – Gwamna Badaru ya ja kunnen Buhari
Gwamnatin jihar Jigawa ta ce ana cigaba da amfani da tsofaffin takardun naira a jihar har zuwa lokacin da kotun koli za ta yanke hukunci.
Kwamishinan yada labarai, wasanni da al’adu na matasa na jihar Bala Ibrahim Mamsa ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa DAILY POST a ranar Alhamis.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ku Yi Siyasa Ba Tare Da Cin Mutuncin Kowa Ba, Tinubu Ya Gargaɗi Magoya Bayan Sa
A cewarsa “Jihar Jigawa na daga cikin jihohin da ke gaban kotun kolin Najeriya CBN kuma kotun ta bayar da umarni “ta hana CBN dakatar ko kayyade ko kuma kawo karshen wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairun 2023 wanda a yanzu haka tsofaffin kuɗin 200, 500 da 1000 na naira maiyuwa ba za su sake zama masu amfani ba.
Ya ce gwamnatin jihar Jigawa ta umurci ‘yan kasar da su daina bijirewa doka da kuma kawo wa al’ummar jihar kunci.
Mamsa ya bayyana cewa ya zo ga gwamnati cewa wasu daidaikun mutane da kungiyoyi a jihar na kin amincewa da tsofaffin takardun kudi na N200, N500, da N1000.
Ya ce gwamnati za ta dauki mataki a kan duk wanda aka samu ya ki amincewa da tsofaffin takardun Naira.
Sai dai kwamishinan ya shawarci jama’a da su kai rahoton duk wani dan kasuwa ko kungiyoyin ‘yan kasuwa da suka ki karban takardun kudi N200, N500, da N1000 a matsayin takardar kudi a jihar Jigawa ga hukumomi mafi kusa.
A wani labarin kuma: Ku Yi Siyasa Ba Tare Da Cin Mutuncin Kowa Ba, Tinubu Ya Gargaɗi Magoya Bayan Sa
Gwamna Umar Abdullahi Ganduje na jihar Kano ya caccaki shugaban kasa Muhammadu Buhari kan kin bin umarnin kotun koli da kuma ci gaba da haramta amfani da tsofaffin kudaden Naira.
A cikin wani faifan murya, an jiyo Ganduje yana tambayarsa cewa, “Ya kamata shugaba Buhari ya tuna cewa sau da dama yana kokarin tsayawa takarar shugaban kasa amma bai samu ba sai da aka yi kawance, amma yanzu bayan ya ji dadin komai sai ya juya baya ga tsarin dimokuradiyyar da ya kai shi ofis”.