Tsohon kakakin majalisar wakilai Yakubu Dogara ya karyata ikirarin cewa, ya koma jam’iyyar APC mai mulki.
Jigo a jam’iyyar PDP a ranar Litinin ya mayar da martani ga tambayar da jaridar DAILY POST ta yi masa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Buhari Ya Taya Xi Jinping Murnar Sake Zabar Sa a Matsayin Shagaban China
“Yana da rikitarwa. Ina goyon bayan ’yan takara ba jam’iyyu ba,” Dogara ya amsa.
Idan ba amanta ba, Dogara ya gana a karshen mako tare da dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar Bauchi, Sadique Abubakar.
Air Marshal Mai ritaya na da shekaru 63, ya kasance babban hafsan hafsoshin sojin Najeriya daga watan Yulin shekarar 2015 zuwa Janairun 2021.
Yan siyasa ne ke zawarcin Dogara saboda ya taka rawar gani wajen kayar da jam’iyyar PDP da APC ta samu nasara a zaben gwamna na 2015.
Ya ba da umarni ga dimbin magoya bayansa, wadanda suka taimaka wa wani jigo a jam’iyyar APC, Jafaru Gambo Leko, ya yi nasara a zaben ‘yan majalisar tarayya da aka yi ranar 25 ga watan Fabrairu.
Matashin dan siyasar ya lashe zaben mazabar tarayya ta Bogoro/Dass/Tafawa Balewa, wadda Dogara ya wakilta daga 2007 zuwa 2019.
Tsohon dan majalisar dai ya koma jam’iyyar PDP ne a shekarar da ta gabata, domin nuna adawa da tikitin takarar musulmi da musulmi na jam’iyyar APC, tsakanin Bola Tinubu da Kashim Shettima.
Sauran wadanda suka yi adawa da hakan sun hada da tsohon sakataren gwamnatin tarayya Babachir Lawal, da Sanata Elisha Abbo, da dai sauransu.
A wani labarin kuma, Yanzu-Yanzu: Lauyoyin Guda Daga Cikin Jam’iyun Adawa, Sun Yi wa Ofishin INEC Diran Mikiya
Biyo bayan rashin gamsuwa da sakamakon zaben shugaban kasa da aka kammala, tawagar lauyoyin jam’iyyar Labour ta isa ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a Abuja domin duba kayan aiki.
Tashar talabijin ta Channels ta rawaito cewa a halin yanzu tawagar na ganawa da jami’an hukumar.