Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party NNPP tayi babban rashi a ranar Talata bayan matakin da shugaban jam’iyyar na kasa Farfesa Rufa’i Ahmed Alkali ya yanke na jagorantar wasu jiga-jigan ‘ya’yanta zuwa jam’iyyar All Progressives Congress APC mai mulki.
Daga cikin wadanda suka sauya sheka sun hada da Sanata Sulaiman Othman Hunkuyi, wanda a lokuta daban-daban ya zama babban sakatarenta da kuma dan takararta na Gwamna a Jihar Binuwai.
Alkali wanda ya taba zama sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa a wancan lokaci, ya ce sun yanke shawarar yin murabus daga jam’iyyar NNPP ne saboda bambance-bambancen daidaikun mutane.
Karanta nanZamu Mayar Da Hankali Akan Sauran Albarkatun Kasa Wadanda Ba Man Fetur Ba-Tinubu
Alkali ya shaida wa mai masaukin baki, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, cewa sun yanke shawarar zaben APC ne a matsayin inda za su biyo bayan tuntubar juna da suka yi, ya kara da cewa duk da cewa PDP ta tuntube shi ya dawo amma cikin girmamawa ya ki saboda dalilan da ya sa ya fice daga jam’iyyar bai canza ba.
Ya ce bayan da kotun koli ta dakatar da duk wasu kararraki da suka shafi zaben shugaban kasa, shugaba Bola Tinubu ya cancanci a ba shi goyon baya da karfafa gwiwar tukin jirgin kasar Najeriya don dawo da fata a kasar.
Bisa la’akari da dimbin kalubalen da kasarmu ke fuskanta a wannan lokaci a tarihin kasarmu, duk ‘yan Najeriya sun cancanci zaman lafiya da kwanciyar hankali don gudanar da rayuwarsu ta yau da kullun. Don cimma wannan, akwai bukatar a kiyaye kasar nan.
Dimokuradiyyarmu tana bukatar a kareta kuma akwai bukatar a tallafa wa wannan Gwamnati,bayan duk wasu kararraki kan zaben shugaban kasa ya kare, lokaci ya yi da ya kamata a ba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu goyon baya.
Yan Najeriya sun dade suna shan wahala har tsawon lokacin da aka bar kasar nan ta yi ta tuhume-tuhume, haka nan kuma sai kara zurfafa radadin da talakawa ke fuskanta a kasarmu.
Da yake mayar da martani, Ganduje ya ce mun san cewa NNPP za ta ruguje kuma yanzu mun ga hakan a fili.
A cewarsa, APC na da kyakkyawan tsari na cikin gida wanda ke samar da daidaito ga dukkan mambobin kungiyar ba tare da la’akari da matsayi ba.
Ganduje ya ce APC cibiya ce mai karfi ta siyasa da ta kunshi mutane masu ilimi da hikima masu fahimtar matsaloli da muradun ‘yan Najeriya.
Shugaban jam’iyyar APC ya bayyana cewa jam’iyyar NNPP ta fi karfi da kyau kafin tsohon gwamnan jihar Kano kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya shigo jam’iyyar.
A wani labarin KumaKungiyar Masu Bukata Ta Musamman Ta Bukaci Hukumar NEDC Take Damawa da ‘Ya’yanta Cikin Lamuranta
Da yake yabawa wadanda suka sauya sheka daga jam’iyyar Ganduje, ya ce an yi tunani sosai kan matakin da suka dauka na ficewa daga jam’iyyar NNPP, inda ya ce ‘ya’yan kungiyar siyasar Kwankwasiyya karkashin jagorancin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso sun yi awon gaba da jam’iyyar tare da gurbata su.
APC jam’iyya ce da ta kware wajen tafiyar da al’amura daban-daban kun dawo inda ya dace. APC za ta kai al’ummar Nijeriya mataki na gaba, ina mai tabbatar muku da cewa a yanzu kun zama cikakkun ‘ya’yan jam’iyyar.
Kun shigo jam’iyyar ne a daidai lokacin da za ku iya taka rawar gani a jam’iyyar. A nan jam’iyyar APC muna gudanar da dimokuradiyyar cikin gida kuma za ku iya neman kowane mukami.