Masu ababen hawa a jihar Kano sun cika da farin ciki daga Jiya Talata zuwa yau, sakamakon kiran da masu gidajen mai suka amsa wajen budewa tare da cigaba da siyar man fetur din.
Wata tawaga ta musamman da ta ƙunshi jami’an tsaron Civil defence sune suka fara wani rangadi a ranar Litinin tare da ɗaukar hukunci mai tsanani kan wanda suka samu da mai kuma ya kulle gidan man.
Wani direban Adaidaita Sahu Auwalu Private ya bayyanawa jaridar Dimokuraɗiyya farin cikinsa, kan kiraye kirayen da kafafen yada labarai suka dinga yi wajen daukar mataki kan masu gidan Man.
Wakilin Jaridar Dimokuraɗiyya a Jihar Kano ya zagaya wasu yankunan jihar domin ganin yadda lamarin yake.
Kuma ya tarar da gidajen mai akan Titin zuwa Gwarzo, kan titin Jami’ar Bayero, Titin Sheik Ja’afar Mahmud Adam da sauran su duk jama’a na cigaba da shiga domin shan mai.
Sannan kuma layukan sunyi sauki domin kuwa cinkoson ƙalilan ne.