By Abbas Yakubu Yaura
Wani jami’in yankin, a ranar Litinin, ya ce akalla mutane bakwai ne suka mutu a lokacin da wani jirgin kasa ya kauce hanya a yankin Kudu maso Gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, wanda shi ne hatsari na biyu a yankin cikin makwanni biyu.
DUBA WANNAN LABARIN: ‘Yan Sanda Sun Damke Wasu Da Ake Zargin Barayin Baburan Adaidaita Sahun Ne A Jihar Rivers
Hadarin ya afku ne a kauyen Buyofwe dake lardin Lualaba a ranar Asabar, A tsakiyar watan Maris, wani jirgin kasa ya fito daga kan titin a kauyen, inda ya kashe akalla mutane 75 tare da raunata 125, a cewar alkaluman binciken hukuma.
“Mutane bakwai ne suka mutu sannan 14 suka samu munanan raunuka” a sabon hatsarin, ministan cikin gida na Lualaba, Deoda Kapenda, ya shaidawa manema labarai ranar Litinin.
“Yawan adadin na iya karuwa saboda adadi mai yawa na fasinja na boye sun makale a karkashin kekunan Jirgin da aka tayar,” in ji shi.
An tattaro cewa an aike da tawagar ceto zuwa wurin da lamarin ya faru cikin gaggawa.
Wani jami’in yankin na kamfanin jiragen kasa ya bayyana cewa, jirgin mai dauke da wagon guda takwas ya taso ne daga garin Tenke dake Lualaba zuwa Kananga a lardin Kasai da ke makwabtaka da tsakiyar kasar.
Ta bar layin dogo a Buyofwe, kimanin kilomita 200 daga Kolwezi, babban birnin lardin Lualaba.
Hanyoyi akai-akai ana karkatar da su a cikin babbar ƙasar Afirka ta Tsakiya. Babu isassun jiragen kasa na fasinja da ƴan hanyoyin sasantawa, don haka mutanen da ke buƙatar yin tafiya mai nisa sukan yi tafiya ta jirgin ƙasa mai ɗaukar kaya.
AFP
Comments 1