Yanzu haka rundunar ‘yan sandan Najeriya ta fara farutar wata yarinya mai suna Fatima Abdullahi Tuge.
A ranar 22 ga watan Afrilu ne rundunar ‘yan sandan kasa Najeriya ta fara farutar Fatima Abdullahi Tuge tare kuma da alkawarin kyautar kudi N250,000 ga duk wanda ya gano mafakar ta ko ya yi sanadiyyar kama ta ya mikawa ‘yan sanda.
An gano cewa Fatima Abdullahi Tuge ‘yar asalin jihar Kaduna ce, kuma kwararriya ce wajen damfara da neman maza, duk namijin da yayi sakaci sha’awa ta debe shi ya kwanta da ita, to babu makawa kwanan sa yazo karshe domin za ta tsaface shi.
Majiyar mu ta ruwaito cewa Fatima Abdullahi Tuge ta dade tana yada labaran karya da batanci a kafar sada zumuntan facebook akan duk wanda ta nemi amincewar sa yaki, daga cikin wadanda Fatima Tuge ta nemi su amince da ita suka ki amincewa harda Hon. Gudaji Kazaure inda shi ma daga karshe ta yi masa sharrin damfara.
Lamarin da yasa Hon. Kazaure ya rika farautar Fatima Abdullahi Tuge da Bindiga zai harbe ta ta gudu jihar Lagos.
Idan za ku iya tunawa Fatima Abdullahi Tuge ce ta yi wani Odiyo a Whatsapp tana yiwa tsohon gwamnan Kano kuma jagoran Kwankwasiyya Rabi’u Musa Kwankwaso da Sule Lamido sharrin cewa Atiku Abubakar ya ba su kudi su yi masa Kamfe sun cinye.
Ko a wannan makon ma Fatima Tuge ta sake yiwa wani bawan Allah mai suna Mustapha Suleiman sharrin damfara kana kuma ta nemi bata rayuwar sa da sihiri shi ma domin yaki amincewa da bukatar ta.
Tuni dai Lauyoyin Mustapha Suleiman sun aike da kwafin takardar karar Fatima Tuge ga Kwamishinan ‘yan sandan kasa reshen birnin tarayya Abuja da kuma jami’an tsaron farin kaya domin a kamo Fatima Tuge ta girbi abinda ta shuka.
Allah shi kyauta, ya kuma kare al’umma daga sharrin shedanun matan zamani.