An kashe ‘yan sanda biyu a yayin da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a hedikwatar ‘yan sanda ta yankin Isu da ke karamar hukumar Isu ta jihar Imo.
Sai dai rundunar ‘yan sandan ta ce ta kama 18 daga cikin maharan.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, CSP Mike Abattam, ya ce wasu mutane dauke da makamai da ake zargin mambobin haramtacciyar kasar Biafra (IPOB) da (ESN) ne suka je tashar a cikin motocin Toyota Sienna guda biyu. Motar Toyota Camry da wasu babura da ba a tantance adadinsu ba, a ranar Lahadi.
Ya ce ‘yan ta’addan sun yi amfani da unguwar da ba a taba gani ba inda suka far wa tashar ta baya, kuma suka rika harbe-harbe suna jefa abubuwa masu fashewa.
Abattam ya ce wutar da ta Tashi ta shafi wasu motoci da wani bangare na ginin sashin.
Ya ce, nan take jami’an ‘yan sanda na sashin suka mayar da martani inda suka budewa maharan wuta.
“Jami’an ‘yan sandan ba su yi kasa a gwiwa ba, inda suka yi wa ‘yan bindigar ruwan wuta, yayin da suke tserewa, wasu kuma suka shiga otal din Golden Suite da Otel Isu Villa.
“Nan da nan aka killace otal-otal guda biyu tare da kai samame, kuma ana cikin haka, an ga jimillar babura 12 da ba su da lambar tantancewa da motoci guda biyu – Lexus RX350 SUV daya da Lexus RX330 SUV guda daya – wadanda ake kyautata zaton ‘yan bindigar ne suka yi amfani da su kuma aka gano su.”
Hakazalika, an kama mutum 17 maza da mata da ake zargin ana yi musu tambayoyi.