Daya daga cikin mai magana da yawun dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, LP, Ndi Kato, ya ce ‘yan Najeriya za su bukaci hutun akalla mako biyu don murmurewa daga hannun gwamnatin Shugaba Buhari.
Sanarwar hakan na kunshe ne a wani sako da ta wallafa a shafinta na Twitter a ranar Asabar.
KU KARANTA: Wasu Kasashe Na Son Koyi Da Matakin Najeriya kan Kamfanin Twitter – Pantami
Idan dai za a iya tunawa dai an yiwa kasar nan Caaa ne sakamakon sake fasalin kudin Naira da babban bankin Najeriya CBN ya sauya.
Wannan dai baya ga matsalar karancin man fetur da ake fama da shi a fadin kasar nan, inda farashin man fetur ya haura N500 a wasu Jihohin kasar.
Sai dai Kato ta fito ta koka kan yadda ‘yan Najeriya suka sha wahala a wannan zamanin.
Ta rubuta cewa, “Lokacin da Buhari ya sauka daga mulki, muna bukatar hutun makwanni akalla 2 domin mu samu murmurewa.
“Yan Najeriya, hakika mun sha wahala.”
A wani labarin kuma: Zan Ci gaba Da Yi wa Tinubu Yakin Neman Zabe — Buhari Ya Sha Alwashi
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sha alwashin ci gaba da yiwa dan takarar shugaban kasa, na jam’iyyar APC Bola Tinubu yakin neman zabe. Kamar yadda Daily Post ta ruwaito.
Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga ‘yan Najeriya yayin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a jihar Nasarawa.