Yanzu-Yanzu: Ƴan Bindiga Sun Yi Kaca-kaca Da Wurin Zaɓe A Legas, Sun Ƙwace Akwatunan Zaɓe
Wasu ‘yan daba sun yi awon gaba da akwatunan zabe a rumfar zabe mai lamba 075 da ke Iyana-Isashi a jihar Legas.
Mazauna yankin sun yi tir da lamarin, inda suka ce an kawo cikas a zaben.
KARANTA WANNAN LABARIN:Zaben Gwamna: Masu kada kuri’a sun yi cirko-cirko kan kan batan ƙuri’ar zaɓe
Ɗaya daga cikin mazauna yankin, Collins Michael, wanda tun farko ya kada kuri’arsa a rumfar zabe, ya shaida wa wakilinmu cewa ‘yan daba sun yi yawa suka kwace akwatunan zabe a lokacin da ake harbe-harbe.
Ya ce, “Muna yin zabe cikin lumana sai muka ji hayaniya ta tashi daga tashar mota. Mutane sun fara gudu ne yayin da ’yan daba suka shigo cikin babura don tarwatsa wannan wuri. Sun kwace akwatunan zabe suka tafi yayin da muke gudu domin tsira.”
Har ila yau, Stanley Ndive, wanda ya kada kuri’arsa a wata rumfar zabe da ke unguwar Shibiri, ya ce ‘yan baranda ne suka yi masa rakiya zuwa rumfar zabe suna nuna masa kwalba a kai tare da tilasta masa kada kuri’ar kin amincewa da zabin da ya yi.
“Sun nuna min kwalba a kai yayin da suke raka ni zuwa rumfar zabe, domin in zabi APC,” inji shi.
Stanley Ndive, wanda ya kada kuri’arsa a wata rumfar zabe da ke unguwar Shibiri, ya ce ‘yan baranda ne suka raka shi rumfar zabe suna nuna masa kwalba a kai tare da tilasta masa kada kuri’ar kin amincewa da bukatarsa.
“Sun nuna min kwalba a kai yayin da suke raka ni zuwa rumfar zabe, domin kada kuri’a ta sabawa burina,” in ji shi.
A wani labarin kuma:Zaben Gwamna: INEC Ta Ja Hankali Kan Masu Katin Shaidar Jabu A Jami’an Tsaro
An daina kada kuri’a a unguwar Ibeku East Ward 1, Unit 020 a karamar hukumar Umuahia ta Arewa a jihar Abia saboda karancin takardar zabe
Shugaban kungiyar, Honarabul Silas Ihemeremadu, da shugaban matasa, Mista Hilary Ochiabuto, wadanda suka yi wa ‘yan jarida jawabi, sun ce sun amince su kauracewa zabe a yankinsu, matukar ba a kawo takardar zabe 60 daga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC.