Mahara sun kai hari kan motar bas din gwamnan jihar Legas da ‘yan jarida a ciki.
An kai harin ne bayan da suka bar fadar Oba Rilwan Akiolu daura da Adeniji Adele.
Daya daga cikin ‘yan jaridan da ke cikin motar, Ayo, ya ce ‘yan bindiga da dama ne suka tare hanyar inda suka rika jifan motar da duwatsu da abubuwa masu hadari.
An farfada gilashin tare da jikkata wasu ‘yan jarida. An kuma lalata motar daukar marasa lafiya da ke gaban ma’aikatan bas din ‘yan jarida.
Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci Oba Akiolu a fadar sa bayan tarbar da shugabanin jam’iyyar da magoya bayansa suka yi masa.