Za mu gurfanar da masu ababen hawan da suke yin lodin kaya – FRSC
Hukumar kiyaye hadurra ta kasa FRSC reshen jihar Ondo, a ranar Lahadin da ta gabata ta bayyana cewa ta kuduri aniyar gurfanar da masu ababen hawa da ke yin sama da fadi a fadin jihar.
Kwamandan hukumar ta FRSC reshen jihar, Mista Ezekiel SonAllah ne ya yi wannan gargadin a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan wani hatsarin daya yi sanadin mutuwar mutum daya tare da raunata mutum takwas a ranar Asabar a jihar.
KARANTA WANNAN LABARIN:Akpabio ya Musanta zuwa Majalissa a makare tare da kawo cikas ga Jadawalin zaman Majalisar
Ya ce duk direban da aka kama shi da abin hawa zai fuskanci hukunci mai tsanani.
A cewarsa, hadarin daya tilo ya faru ne sakamakon fashe tayar wata mota da ta cika da yawa.
Hatsarin ya faru ne da misalin karfe 4:12 na yamma a mahadar Amurin da ke kan titin Owo/Akure a karamar hukumar Owo ta jihar.
Shugaban FRSC ya bayyana cewa motar, Toyota Hiace da fasinjoji tara ta yi hatsarin da ya yi sanadin mutuwar mutum daya a nan take.
SonAllah ya ce an kai wadanda lamarin ya rutsa da su zuwa cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke Owo, domin yi musu magani, yayin da aka mika motar da kayanta ga ofishin ‘yan sanda na Uso.
“A matsayinka na fasinja, idan ka san cewa motar ta wuce lodi kuma kana darajar rayuwarka, ba kwa buƙatar shigar da irin wannan motar,” in ji shi.