By Abbas Yakubu Yaura
‘Yan takarar shugaban kasa bakwai da suke fafatawa a karkashin inuwar jam’iyyar APC sun yi watsi da sunayen mutane biyar da aka ce an mika wa shugaban kasa Muhammadu Buhari domin ya zabi dan takarar yarjejeniya.
Sun dage cewa ba wanda ya tuntube su kafin gwamnonin su kai ga yanke wannan shawara.
Masu fafutukar ganin sun yi wannan ikirarin ne a wata sanarwa da suka fitar da sanyin safiyar Talata.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ciki Ya Duri Ruwa Yayin Da Wakilai 2,322 Zasu Zabi Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar APC
‘Yan takarar sun hada da Gwamnan Kuros Riba, Ben Ayade; Tsohon Ministan Ilimi Emeka Nwajiuba; Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Ogbonnaya Onu; tsohon gwamna Rochas Okorocha da dan kasuwa Tein Jack-Rich.
Masu neman takarar dai sun ce shugaba Buhari bai fito fili ya goyi bayan mayar da kujerar shugaban kasa zuwa Kudu ba tare da nuna shakku kan manufar gwamnonin.
Umarnin Shugaban kasa abu ne mai sauki, cewa duk masu neman Shugabancin kasa har da na Arewa su hadu su daidaita domin a samar da dan takara daya.
A halin yanzu ba a tuntube mu ba ko kuma halartar wani taro inda aka amince aka aika wa shugaban kasa irin wadannan sunaye,” sanarwar ta kara da cewa.
Onu ya kara da cewa, “Muna kuma da cikakken ikon cewa yawancin wadannan Gwamnonin an yi musu alkawari tare da ba su wasu nau’o’in jin dadi don dakile wannan tsari domin a baiwa mutum daya mai takara kuma irin wannan babban makircin zai yi kasa a gwiwa.
“Moreso, jam’iyyar da Sanata Abdullahi Adamu ke jagoranta, ita ce babbar hukumar jam’iyyar inda za a sanar da yanke shawarar da masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar suka yanke, kuma za a aiwatar da su, idan babu wannan yunkuri ya zama banza.”
Sunayen da aka mika wa Buhari sun hada da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, jagoran jam’iyyar APC na kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi, tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi da kuma gwamna Dave Umahi na jihar Ebonyi.