By Abbas Yakubu Yaura
Kungiyar sadarwa ta jihar Zamfara ta ce wasu ‘yan bindiga sun sace mambobinta sama da 30 a ranar Asabar a hanyar Sokoto zuwa Gusau.
Sakataren yada labarai na kungiyar, Malam Ashiru Shaibu Zurmi ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Gusau ranar Lahadi.
KARANTA WANNAN LABARIN: Shugabancin Kasa 2023: Abinda Yasa Kwankwaso, Peter Obi Ba Zasu Iya Kayar Da Atiku, Tinubu Ba – Adeyanju
Ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da ‘yan kungiyar ke komawa Gusau bayan halartar daurin auren daya daga cikin mambobinsu a jihar Sokoto.
Sai dai ya ce 11 daga cikin wadanda abin ya shafa sun yi sa’a sun tsere da raunuka daban-daban, yayin da sama da 30 a ke ci gaba da tsare su .
Don haka, ya yi kira ga gwamnatocin Jihohi da na Tarayya da su sanya ido kan halin da suke ciki tare da ceto rayukan wadanda abin ya shafa cikin gaggawa.
“Dukkan wadanda abin ya shafa sun kasance matasa ne wadanda ba za a iya auna gudummuwarsu ta yau da kullun ga tattalin arzikin kasar ba,” in ji shi.
“Dukkan mu shaida ne kan dimbin albarkatun da aka yi a lokacin zabukan fitar da gwani na jam’iyyar da bangarorin biyu suka yi. Don haka muna kira da a dauki irin wannan alkawari domin ceto rayukan wadannan matasa.”
Ya yi nuni da cewa kowanne daga cikin wadanda abin ya shafa yana da akalla ma’aikata 10 a karkashinsa.
Comments 1