Zargin wawure 37bn: Ministar Buhari ta yi watsi da sammacin EFCC
Sadiya Umar-Farouq, tsohuwar ministar harkokin jin kai da kula da bala’o’i da ci gaban al’umma a zamanin tsohuwar gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, ta ki amsa gayyatar da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, inda ake zargin ta da karkatar da naira biliyan 37.1 a lokacin da take kan mulki ta hanyar dan kwangila, James Okwete.
A baya dai Majiyar Jaridar Dimokuradiyya ta rahoto cewa ana sa ran tsohuwar Ministar zata gurfana a gaban EFCC inda zata amsa tambayoyi a babban ofishin hukumar a ranar Laraba da misalin karfe 10:00 na safe a Abuja.
KARANTA WANNAN LABARIN:Ko kuyi wa jiha aikin da ya dace, ko in kore ku daga aiki – Adeleke ga muƙarrabansa
Sai dai wata majiya ta EFCC da ta yi magana a boye ta tabbatar da cewa Sadiya Umar-Farouq ta ki gayyatar hukumar a ranar Laraba.
“Mun rufe daga aiki yanzu saboda ba ta zo yau ba, kuma yanzu karfe 6 na yamma ne. Yana da tabbacin cewa ba za ta taɓa fitowa a yau ba. ”
Wannan ci gaban dai na zuwa ne sa’o’i 24 bayan shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da Halima Shehu, ko’odinetar hukumar kula da harkokin zuba jari ta kasa, saboda hannu a cikin wannan zamba.
Saboda haka EFCC ta kama Halima Shehu
A wani labarin kuma:Masu Zuwa Nan Gaba, Babu Abinda Za Su Yi, Sai Biyan Bashin Najeriya – Obasanjo
A ranar Laraba tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya ce rashin gudanar da mulki da gwamnatocin baya suka yi ya tilastawa Najeriya tarin basussuka da za su yiwa ƴan ƙasar illa.
Wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Kehinde Akinyemi, ya fitar ta nuna cewa, dattijon ya yi magana ne a lokacin wata ganawa da masu bayar da lambar yabo ta 2023 na Future Africa Leaders Foundation, wani shiri na Fasto Chris Oyakhilome.