- Gwamna Uba Sani ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin Harin Daya hallaka Mutane tare da Jikkata Wasu da dama
- Bayan ya samu labarin asarar rayuka da jikkatar wadanda abin ya shafa,gwamnan ya ce bincike cikin gaggawa zai hana faruwar al’amura irin hakan a nan gaba
- Tuni gwamnatin Jihar ta ce za ta dauki nauyin kula da duk wadanda abin ya shafa
Biyo bayan ikirarin da sojojin Najeriya suka yi na kai harin bam da aka kai kan mazauna kauyen Tudun Biri sama da 30, Gwamna Uba Sani ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.
A wata sanarwa da Muhammad Lawal Shehu, babban sakataren yada labarai na gwamnan jihar Kaduna, ya fitar, ta ce Gwamna Sani wanda ya kadu bayan ya samu labarin asarar rayuka da jikkatar wadanda abin ya shafa, ya ce bincike cikin gaggawa zai hana faruwar al’amura a nan gaba.
KARANTA WANNAN: Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Benue ta Yi Watsi da Gargadin Majalisar Dattawa, ta Tabbatar da Kwamitocin Riko
“Na ba da umarnin gudanar da bincike cikin gaggawa kan lamarin. Mun kuduri aniyar hana sake afkuwar wannan bala’i tare da tabbatar wa al’ummarmu cewa za a ba da fifiko wajen kare su a ci gaba da yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan fashi da sauran miyagun laifuka.
“Na kuma ba da umarnin kwashe wadanda suka jikkata cikin gaggawa zuwa asibitin koyarwa na Barau Dikko domin samun kulawar gaggawa.
“Gwamnati ce za ta dauki nauyin kula da su da kayan aikin da suka shafe su,” in ji Gwamna Sani.
A yayin da ya ke kira da a kwantar da hankulan al’ummomin da abin ya shafa, ya bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da bincike da ceto a yankin, ya kara da cewa gwamnatin jihar ta aike da manyan jami’an gwamnati zuwa yankin domin duba halin da ake ciki, da kuma kaiwa ga iyalan wadanda abin ya shafa tare da ba gwamnati shawara kan matakan gaggawa da matakan da ya kamata a dauka don rage radadi ga iyalan wadanda abin ya shafa.
“Gwamnatin jihar Kaduna ta yi nadamar asarar rayuka da aka yi, kuma ta jajirce wajen ganin mazauna yankin sun ci gaba da rayuwa tare da gudanar da sana’o’insu na halal ba tare da tsoro ba,” inji Gwamnan.
A wani labarin kuma, Mataimakin Shugaban Majalisa, Kalu Ya Gargadi Matasa Game da Garkuwa da Mutane, Tayar da Zaune Tsaye
Mataimakin kakakin majalisar wakilai, Hon. Benjamin Okezie Kalu, ya bukaci matasan Najeriya da su bayar da gudunmawa mai ma’ana ga ci gaban kasa
A cewar Kalu yanzu ne lokacinku ya ku matasan Nijeriya, ku kwaci rigar shugabanci, ku ci gaba da yin tattaki zuwa kyakkyawar makoma
Ya zama wajibi “Ku shiga fagen jagoranci, ba a matsayin mahalarta kawai ba amma a matsayin masu tsara sabuwar Najeriya
Mataimakin kakakin majalisar wakilai, Hon. Benjamin Okezie Kalu, ya bukaci matasan Najeriya da su bayar da gudunmawa mai ma’ana ga ci gaban kasar, yana mai cewa lokaci ya yi da za su gina kasar da burinsu.
Hon. Kalu ya yi wannan bukatar ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen kaddamar da tallafi na Asusun Matasa na Najeriya (NYFF). Taken shi ne ‘Catalysing Youth Agency for the Nigeria we want,’