- Gwamnan Ondo Lucky Aiyedatiwa ya dakatar da shugabannin riko na kananan hukumomi 18, da LCDAs 33
- Kafin dakatarwar wata babbar kotu ta bayar da umarnin wucin gadi da PDP ta shigar na neman hana marigayi Gwamna Akeredolu kaddamar da duk wani mutum da ba a zaba ta hanyar dimokradiyya ba
- Matakin dai bai yiwa wadanda aka dakatar dadi ba
Gwamna Lucky Aiyedatiwa na jihar Ondo ya dakatar da shugabannin riko na kananan hukumomi 18, da LCDAs 33 na kananan hukumomin jihar.
Aiyedatiwa ya ce za a ci gaba da dakatar da shugabannin riko har sai wata kotu ta yanke hukunci kan lamarin.
KARANTA WANNAN: Ministar Jin Kai ta Ziyarci Wadanda Suka Tsira a Harin Filato
A wata wasika mai dauke da sa hannun Alonge Adewale na ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu, gwamnan ya umarci shugabannin riko da aka dakatar da su mika duk wasu kadarori na LCDC.
Wasikar ta kasance kamar haka: “Ta zo ga ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu cewa duk da dakatar da daukacin mambobin kwamitin rikon kwarya na kananan hukumomi da na (LCDAs) na Kananan Hukumomin da aka nada kwanan nan a jihar ta hanyar wani aiki, kotun da ke da hurumin shari’ar, wasu mutanen da ke cikin wadannan tsoffin mukamai na ci gaba da nuna kansu a waccan mukamai.
“Saboda haka, an umurce ni da in nemi shugabannin kananan hukumomi (HOLGAs) na dukkanin kananan hukumomin da su gaggauta daukar nauyin shugabancin kananan hukumominsu/ LCDAs wajen gudanar da aiki har zuwa lokacin da za a warware dukkan batutuwan da suka shafi shari’a kan wannan batu.”
Wata babbar kotun Akure a karkashin mai shari’a Yemi Fasanmi ta bayar da umarnin wucin gadi da jam’iyyar PDP ta shigar na neman hana marigayi Gwamna Rotimi Akeredolu kaddamar da duk wani mutum ko mutanen da ba a zabe su ta hanyar dimokradiyya ba a matsayin mamba na kwamitocin riko, gudanar da al’amuran kananan hukumomi da LCDAs, har zuwa lokacin da za a yanke hukunci a cikin karar.
Daga baya mai shari’a Fasanmi ya hana shugabannin riko aiki bayan sun koma aiki bisa uzurin rantsar da su kafin a ba da umarnin.
A wani labarin kuma, NiMET ta Yi Wani Gargaɗi Ga Masu Fama da Asma, Ma’aikatan Jirgin Sama
Hukumar NiMet ta fitar da sanarwar taka tsantsan ga mutanen da ke fama da cutar asma
“Ya zama wajibi ga mutanen da ke fama da cutar asma da sauran matsalolin numfashi da su yi taka tsantsan game da yanayin”
Ana sa rana samun yuwuwar saukar ruwan sama da tsawa a wasu sassan Najeriya
Hukumar kula da yanayi ta Najeriya NiMet ta fitar da sanarwar taka tsantsan ga mutanen da ke fama da cutar asma da ta numfashi.
An kuma bayar da gargadin ne game da kurar hazo da gajimare da ke tafe ga ma’aikatan Jiragen Sama.