- Gwamnatin Oyo ta bukaci a kwantar da hankula sakamakon fashewar wani abu da ta afku
- Wannan na zuwa ne bayan wata girgiza da ta afku a Ibadan
- Jami’an tsaro na gudanar da bincike domin gano asali da kuma dalilin faruwar lamarin
Gwamnatin Oyo ta bukaci a kwantar da hankula sakamakon fashewar wani abu da ta afku a Old Bodija, kusa da titin Adeyi da Dejo Oyelese da ke Ibadan, a yammacin ranar Talata.
An shawarci mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu yayin da jami’an tsaro ke gudanar da bincike domin gano asali da kuma dalilin faruwar lamarin.
KARANTA WANNAN: Da Dumi-Dumi: Mazauna Ibadan Sun Firgita Yayin Da Kasa Ta Girgiza
“Gwamnatin jihar Oyo tana sane da rahoton fashewar wani abu a Ibadan.
Saboda haka “an yi kira ga jama’a da su kwantar da hankulansu domin jami’an tsaro na gudanar da bincike domin gano madogara da musabbabin faruwar lamarin.”
Duk da haka, akwai bidiyoyi a yanar gizo, da ke nuna gizagizai masu ƙura, kona gidaje, da motoci, kamar yadda fashewar ta yi ta yawo a dandalin sada zumunta daban-daban.
Gwamnatin ta kara da cewa hukumomin da abin ya shafa na gudanar da aikin bincike da ceto a wurin da lamarin ya faru, da suka hada da dukkan shugabannin jami’an tsaro da na ‘yan sanda da kuma jami’an kashe gobara.
Gwamna Seyi Makinde yana son kowa ya nutsu kuma ya tabbata ana kula da bukatunsa da lafiyarsa.
A wani labarin kuma, Kasar Namibia Ta Lallasa Tunisia da Ci 1-0 Mai Ban Haushi a Gasar AFCON 2024
Kasar Namibia ta zura kwallo daya tilo a wasan inda ta girgiza kasar Tunisia mai matsayi na daya a rukunin E
Sakamakon ya bai wa kungiyar damar fitowa fili
Ana kyautata zaton ita ce kungiya mafi rauni a cikin rukunin
Kasar Namibia ta zura kwallo daya tilo a wasan inda ta girgiza kasar Tunisia mai matsayi na daya a rukunin E na farko a gasar cin kofin nahiyar Afirka AFCON 2024 da ake cigaba da Yi.
Ana kyautata zaton ita ce kungiya mafi rauni a cikin rukunin, ya kamata a yi yawo a wurin shakatawa ga wadanda suka yi nasara a shekarar 2004.