Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi a ranar Alhamis ta ce, ba a samu asarar rai ba, yayin rikicin da ya barke tsakanin al’ummomin kan iyakar a jihar da kuma Gombe.
Kakakin rundunar ‘yan sanda a jihar, Ahmed Wakil ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Bauchi, yayin da yake mayar da martani kan rahotannin kashe -kashen da aka ce an yi, bayan wasu al’ummomin Gombe sun mamaye wasu gonakin da ke karamar hukumar Ganjuwa na jihar Bauchi.
Wakil ya bayyana cewa, maharan sun yi harbi a sama, sun lalata gonaki sannan suka tafi.
Ya Kara da cewa, daga rahoton da rundunar ta samu, babu wanda aka kashe a harin.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ganduje ya yaba da aikin Hisbah, Zai kara Musu Albashi
Kazalika ya ce ce rundunar ta tura da jami’ai zuwa wurin kuma tuni al’amura suka dawo dai-dai a yankin.
A wani labarin Kuma na daban.
Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta ce, ta cafke wasu mutane shida da ake zargi masu garkuwa da mutane ne da suka kai hari ofishin’ yan sanda na Ngurore da ke Yola ta Kudu, kuma suka yi garkuwa da wata uwa.
Kamfanin Dillancin Labaran Kasa NAN ya ruwaito cewa, lamarin ya faru ne a ranar 10 ga watan Oktoban shekarar nan, kuma an ceto wadanda abin ya shafa.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mista Mohammed Barde ne ya bayyana hakan, yayin wata ziyarar ban girma da kwamitin hulda da jama’a na‘ yan sandan Adamawa (PCRC) ya Kai shalkwatar rundunar a yau Alhamis a garin Yola Babban Birnin jihar.
Ya ce rundunar a shirye take don magance duk wani aiyukan garkuwa da mutane, fashi da makami, da sauran ayyukan laifi fadin jihar.
Barde ya yi kira da a ci gaba da ba kwamitin goyon baya ta hanyar ba da bayanai masu amfani ga ‘yan sanda, don tabbatar da zaman lafiya da tsaro a fadin kananan hukumomi 21 na jihar.
Ya ba su tabbacin cewa za a tafiyar dda irin wadannan bayanai cikin sirri.
Kwamishinan ya shawarci Kwamitin na PCRC da su ci gaba da kasance wa masu hadin kai, wajen gudanar da ayyukansu da kuma wasu bangarori daban -daban.
Mista Olu Adegoke, Shugaban Kwamitin PCRC na Jiha, ya ba Barde tabbacin cikakken goyon baya da haɗin kai don tunkarar ƙalubalen tsaro a jihar.