By Abbas Yakubu Yaura
Rundunar sojin Najeriya a ranar Juma’a ta gargadi masu ruruta wutar rikici a wurare daban-daban a fadin kasar dasu daina ayyukan rashin kishin kasa, tana mai cewa nan ba da dadewa ba za a yi musu hukunci mai tsauri.
Babban Hafsan Sojoji (COAS), Lt.Janar Faruk Yahaya, shine wanda ya yi wannan gargadin a Abuja a wajen rufe taron shekara-shekara na COAS na shekarar 2021, ya kuma tabbatar wa ‘yan Nijeriya alamun inganta tsaro a fadin kasar nan a shekara mai zuwa.
Gargadin na Yahaya ya zo ne sa’o’i kadan bayan zanga-zangar da ta barke a wasu jihohin Arewacin kasar nan kan kashe-kashen da aka yi a Sakkwato da Katsina da kuma rashin tsaro a kasar baki daya.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aike da wata tawaga ta musamman wadda ta kunshi shugabannin hukumar leken asiri da tsaro ta kasa zuwa jihohin Sokoto da Katsina domin mayar da martani kan yawaitar hare-haren ‘yan bindiga.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa da yake jawabi a yayin taron, hafsan sojojin ya sha alwashin cewa rundunar sojin zata yi duk abin da doka ta tanada domin shawo kan matsalar tsaro, yana mai kara cewa sojoji za su ci gaba da tabbatar da cewa ‘yan kasa masu son zaman lafiya sun gudanar da sana’o’insu na halal da kuma gudanar da rayuwarsu ba tare da tsoro ko fargaba ba, ko kuma cin zarafi.
Kazalika Yahaya ya umurci kwamandojin cibiyoyin horar da sojoji dasu tabbatar da horar da jami’ai da sojoji da kwarewa don tunkarar duk masu aikata laifuka a wurare daban-daban.