Gwamnan jihar Gombe Muhammad Inuwa Yahaya ya rantsar da mai shari’a Joseph Awak a matsayin sabon babban Alkalin riko na jihar.
Rantsar da Joseph Awak ya biyo bayan ritayar mai shari’a Mu’azu Abdulkadir Pindiga ne a ranar 1 ga watan Janairu.
A nasa jawabin, Gwamna Yahaya ya bukaci babban alkalin ya yi adalci ga kowa da kowa ba tare da nuna bambanci, tsoro ko son zuciya ba.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ya jaddada goyon bayan gwamnatinsa ga bangaren shari’a da ‘yan majalisa wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu yadda ya kamata domin amfanin al’ummar jihar Arewa maso Gabas baki daya.
“A namu bangaren, wannan gwamnatin za ta ci gaba da baiwa bangaren shari’a da ‘yan majalisa goyon baya wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu yadda ya kamata domin amfanin al’ummar jihar Gombe baki daya,” inji shi.
“Bari na sake nanata cewa muradin wannan gwamnati ce ta samu daidaiton alakar aiki da bangaren shari’a da na majalisar dokoki; Dole ne bangarori uku na Gwamnati su hada kai don ci gaban jihar mai kauna da matasan kasarmu, ko shakka babu hadin kan mu shine karfinmu.”
Yayin da yake yabawa mai shari’a Awak bisa mukaminsa na mukaddashin CJ, Gwamna Yahaya ya kuma yabawa tsohon babban alkali , Mai shari’a Mu’azu Pindiga bisa hidimar da ya yi wa jihar.