Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da mai shari’a Olukayode Ariwoola a matsayin babban jojin Najeriya, CJN.
An rantsar da Ariwoola a ranar Litinin a zauren majalisar da ke Abuja.
Ya karbi mulki daga hannun tsohon CJN, Ibrahim Tanko Muhammad wanda ya yi murabus a ranar Litinin saboda rashin lafiya.
An haifi Mai shari’a Ariwoola ne a ranar 22 ga watan Agustan shekarar 1958 kuma a halin yanzu shi ne babban alkalin kotun koli.
Tsohon Alkalin Kotun Daukaka Kara ne kuma an daukaka shi zuwa Kotun Koli bayan sauya shekarsa daga Babbar Kotun Jihar Oyo.
Ariwoola ya fara karatunsa ne a garinsu Iseyin a makarantar Muzahara ta karamar hukumar Oluwole a karamar hukumar Iseyin ta jihar Oyo tsakanin shekarar 1959 zuwa 1967.
A WANI LABARIN KUMA Kutu Ta Tasa Keyar Wani Mutum Zuwa Gidan Yari, Bisa Zargin Yin Luwadi Da Wani Yaro
Wata Kotun Majistare da ke Kano a ranar Litinin ta ba da umarnin tsare wani matashi dan shekara 30, Abdullahi Idris, da ake zargi da yin lalata da wani yaro dan shekara 13, a gidan gyaran hali har sai an ba da shawarar kan shari’a.
Idris wanda ke zaune a Sheka Baranda Quarters Kano, ana tuhumar sa ne da laifin yin garkuwa da yaton da kuma wani laifi da bai dace ba.
Alkalin kotun, Mustapha Sa’ad-Datti, ya umurci ‘yan sanda da su mayar da kundun shari’ar Idris zuwa ofishin daraktan kula da kararrakin jama’a na jihar Kano domin samun shawarwari kan shari’ar.
Sa’ad-Datti ya dage ci gaba da shari’ar har zuwa ranar 2 ga watan Agusta domin karin bayani.
Tun da farko, Lauya mai shigar da kara, Ms Asma’u Ado, ta shaida wa kotun cewa Idris ya aikata laifin ne a ranar 11 ga watan Fabrairun 2022 a Sheka Baranda Quarters Kano.
Ado ya yi zargin cewa da misalin karfe 10 na dare Idris ya yaudari yaron mai shekaru 13 a cikin dakinsa da ke Sheka Baranda Quarters Kano inda ya yi lalata da yaron.
Laifin, in ji ta, ya saba wa tanadin sashe na 272 da 284 na kundin laifuffukan jihar Kano.
Sai dai rahotonni sun bayyana cewa, Idris ya musanta aikata laifin da ake zarginsa da shi.