Wata mata ‘yar shekara 27 mai suna Misis Cynthia Agho ta kashe kanta a garin Benin babban birnin jihar Edo.
An ruwiato cewa an samu matar tana rataye akan wata igiya daure a wuyanta ga fanfo a cikin dakin kwananta.
Rahotanni sun kuma bayyana cewa lamarin ya faru ne a unguwar Lucky Way da ke Aduwawa a cikin birnin Benin.
Inda kuma wasu rahotannin suka bayyana cewa an kama mijin matar, Emmanuel Omoru, biyo bayan rade-radin da ake yi na cewa ya kashe matarsa amma ya yi basajan cewa ita ta kashe kanta.
Sai dai kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Edo, Chidi Nwanbuzor, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce, “Wadda ake zargin ta kashe kanta ne, a ranar 7 ga watan Yuli, ofishin ‘yan sanda na Aduwawa ya samu kiran waya cewa wata mata ta kashe kanta ta hanyar rataya a gini mai lamba 10, titin Omozese, wajen Lucky Way. Aduwawa dake binin Benin.”
Nwanbuzor ya ce a lokacin da ‘yan sandan suka ziyarci wurin da abun ya faru, sun hadu da wata mata da ta gano mijin marigayin, Emmanual Omoru; Har ila yau, ta bayyana wanda aka kashen da Misis Cynthia Agho, mai shekaru 27, wacce ta zargaye kanta da igiya da aka daure da fanfo a cikin dakin kwananta.
“An samu wata kujera a karkashin fankar rufin, an dauki hoton gawar, an sauke ta zuwa dakin ajiye gawa na ‘yan sanda don binciken gawarwakin. Ba a sami rubutaccen rubutu a wurin ba.” inji Kakakin rundunar.
A cewarsa, an fara gudanar da bincike domin gano ko lamarin da ake zargin kashe kanta ne ta yi, ko kuma kisan kai ne wani ya aikata.
“Jita-jita na yawo cewa lamari ne da ake zargin kisan kai ne kuma shi ya sa aka fara bincike don gano gaskiyar,” in ji Nwanbuzor.
Ya kara da cewa, “Mijin nata yana hannun ‘yan sanda ana gudanar da bincike a ofishin ‘yan sanda na Aduwawa kuma za a tura shi sashin binciken manyan laifuka na rundunar domin yin cikakken bincike.