Daga: Abbas Yakubu Yaura
Hukumar da ke kula da ayyukan ‘yan sanda (PSC) ta dakatar da daukar sabbin jami’an ‘yan sandan Najeriya.
Hukumar ta yi hakan ne kasa da sa’o’i 24 da babban sufeton ‘yan sandan Najeriya, Usman Baba, ya fusata kan wani tallata daukar aiki.
KARANTA WANNAN LABARIN: 2023: PDP Ba Jam’iyyar Bangaranci Ba Ce, Bai Kamata Arewa Ta Kwashe Komai Ba – BoT
A wata sanarwa da kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, IGP ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi watsi da tallan da aka sanya a cikin jaridun kasar.
Da take mayar da martani a ranar Talata, hukumar a cikin wata sanarwa da kakakinta, Ikechukwu Ani, ya fitar ta tabbatar da cewa akwai batutuwa tsakanin rundunar ‘yan sanda da hukumar, inda ta ce za a daidaita al’amura da wuri.
Ya roki ‘yan Najeriya da suka nuna sha’awar shiga cikin ayyukan rundunar da kada su nemi aikin har yanzu domin baiwa hukumar lokaci ta sasanta rikicin da ke tsakaninta da hukumomin ‘yan sanda.
Ani ya ce: “Hukumar ‘yan sanda ta lura da yadda rundunar ‘yan sandan Najeriya ta buga game da aikin daukar ma’aikata na 2022. ‘Hukumar na son bayyana cewa, za a warware duk wasu batutuwan da suka shafi wannan aiki a tsakanin bangarorin biyu domin maslahar kasa.”
“Duk masu sha’awar neman aiki da sauran ‘yan Najeriya masu son yin aiki a rundunar ‘yan sandan Najeriya su yi hakuri yayin da ake magance wadannan matsalolin.”
“Hukumar za ta ci gaba da kokarin baiwa ‘yan Najeriya ‘yan sandan da za su yi alfahari da su.”
Daily Trust ta tuna cewa a baya Hukumar PSC ta kai karar Hukumar NPF da kuma tsohon Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda, Mohammed Adamu, bisa laifin gudanar da ayyukan daukar ‘yan sanda 10,000 a shekarar 2019, amma daga baya aka shawo kan lamarin.
Rashin jituwar da aka samu a wancan lokacin shine ko alhakin hukumar PSC ko NPF ne ta tafiyar da tsarin daukar ma’aikata.
A wani labarin kuma Yan sanda sun kama ASP na bogi a Akwa Ibom
Rundunar ‘yan sandan jihar Akwa Ibom ta ce ta kama wani mutum mai suna Vincent Sampson Enuneku da ke bayyana kansa a matsayin mataimakin Sufeton ‘yan sanda wajen aikata munanan ayyuka a jihar.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Odiko Macdon ya fitar kuma wakilin Majiyar jaridar Dimokuradiyya a Uyo ya samu a ranar Talata, ta ce wanda ake zargin dan shekara 43 daga karamar hukumar Ndokwa ta jihar Delta, ya yi kaurin suna wajen gabatar da shaidar karya na aikin dan sanda, a wuraren bincike yayin da kuma ya ke jigilar tabar wi-wi da sauran abubuwan da aka haramta a cikin jihar.