Gwamnatin Legas ta yi gargaɗin cewa za ta kafa dokar kulle idan har mutane suka ci gaba da saba sharuddan da aka shata bayan sassauta dokar fita
Gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu ya ce duk da aikin faɗakar da al’umma da aka yi amma abin takaici sai ka ga dandazon jama’a a bankuna da kasuwanni a sassan jihar suna saɓa ƙa’ida.
Ya kuma ce za a kama duk ɗan okada da kuma motocin fasinja da ke zirga-zirga idan suka ci gaba da saɗa dokokin da aka shata.