An Sake samun karin mutum sha shida da suka warke daga cutar Korona a jihar Kano. Gwamnatin Kano din ne ta sanar da sallamar karin mutane 16 daga cibiyoyin killace masu fama da Korona, bayan da gwaji har sau biyu ya tabbatar da cewa sun warke daga cutar.
Cikin sanarwar da ya rabawa manema labarai cikin karshen makon nan a garin Kano, Kwamishin yada labaran jihar Muhammad Garba ya ce karin wadanda aka sallamar ya sanya adadin wadanda suka warke daga annobar Korona a Kano suka kai 22.
Bayanai sun ce cikin karin mutanen da aka sallama akwai Kwamishinan lafiyar Kano Dakta Aminu Ibrahim Tsanyawa da kuma mataimakin shugaban kwamitin yakar cutar Korona a Jihar Farfesa Abdulrazak Garba Habeeb.