Masu sana’ar Okada da jami’an hukumar kula da ababen Hawa ta jihar Legas, wadanda ke aiwatar da dokar hana Okada a jihar sun yi arangama a ranar Talata.
Majiyoyi da dama a shafukan sada zumunta sun gargadi matafiya da mazauna yankin da su yi taka tsantsan a kewayen yankin
Sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Legas, Benjamin Hundeyin, ya yi ikirarin cewa yankin na cikin hadari.
Jaridar PUNCH ta tattaro cewa yan Okada da suka yi ta’adi sun lalata motoci a yankin.
Da take mayar da martani kan lamarin, PPRO na Legas ya ce, “Idi-Araba yana zaune lafiya. Babu abin damuwa. Wasu ma’aikatan babur ne kawai suke kokarin tayar da hankali bayan an kama baburan su.
“Mutanenmu sun Isa wurin. Kwamishinan ‘yan sanda Abiodun Alabi da kan sa shi ke daidaita lamarin.
“Ba za su iya yin faɗa ba saboda hukumar kula a ababen Hawa ta jihar Legas ta shirya sosai.
“Sun yi ta faruwa ne bayan da hukumar ta kama wasu babura. An shirya rundunar kwantar da tarzoma domin tabbatar da doka da Oda a yankin. Babu shakka babu abin damuwa a kai.” Inji Kakakin rundunar Yan sandan jihar.
A wani labari Kuma na daban.
Alhaji Isa Baba Buji, daya daga cikin wakilan jihar Jigawa a babban taron jam’iyyar APC na musamman da ke gudana a Abuja ya rasu.
Majiyar Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito cewa Buji ya rasu a babban birnin tarayya Abuja a ranar Talata.
Har zuwa rasuwarsa kwatsam, Buji ya kasance mataimakin shugaban jam’iyyar APC mai kula da jihar Jigawa ta kudu.
Rahotanni sun bayyana cewa, ya kwana da safe a ofishin hulda da jama’a na Kasa da ke Babban Birnin Tarayya Abuja, a lokacin da yake shirin zuwa wurin taron.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, jami’in hulda da jama’a na jam’iyyar APC reshen jihar Jigawa, Bashir Kundu, ya shaida wa Jaridar Daily Trust cewa, “Tabbas ya rasu da safiyar yau”.
Jami’in hulda da jama’an ya kara da cewa “ya fadi a ofishin hulda da jama’a na jihar Jigawa da ke Abuja, inda aka garzaya da shi asibiti ya rasu kafin a isa asibitin. Da muka isa asibitin, an tabbatar da rasuwarsa.”