- Tsohon gwamnan Ribas, Nyesom Wike ya bayyana abin da zai yi idan Tinubu ya ba shi mukami.
- Jagoran gwamnonin G5 ya ce zai tuntubi matarsa da abokansa idan Tinubu ya bashi mukami.
- Wike yace zai tantance kansa idan ya shirya. Ba zai taba yin abin da bai shirya ba.
Tsohon gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike ya bayyana abin da zai yi idan shugaba Bola Tinubu ya ba shi mukami.
Daily Post ta rawaito cewa Wike ya ce zai tuntubi matarsa da abokansa idan Tinubu ya bashi mukami.
KARANTA WANNAN: Ban Taba Cin Zarafin Matata Ba – Wani Mataimakin Gwamna
Da yake magana da BBC Pidgin, jigon jam’iyyar PDP, ya kuma lura cewa yana son ya huta bayan ya yi gwamna na tsawon shekaru takwas.
A cewar Wike: “Zan huta; Na yi aiki tsawon shekara takwas, don haka zan huta.
“Tinubu bai sanar da ni ba game da samun wani mukami; Ni ban kai girman bautar kasata ba, amma bai taba fada min cewa zai ba ni mukami ba.
“Idan ya tambaye ni, abu na farko da zan fara yi shi ne na tambayi matata da abokai meye ra’ayinsu game da lamarin.
“Nima zan tantance kaina idan na shirya. Ba zan taba yin abin da ban shirya ba.”
A wani labarin kuma,’ Yan Sanda Sun Ceto Wasu Yara Tara Da Aka Sace A Zamfara
Rundunar ‘yan sandan Zamfara ta bayyana cewa ta ceto yara tara da ‘yan bindiga suka sace.
A ranar 3 ga watan Yuni, 2023 an samu labari sace yara tara da suka hada da maza da mata.
Da samun rahoton, rundunar ‘yan sandan hadin gwiwa da sauran jami’an tsaro sun tattaru zuwa wurin da lamarin ya faru.