Daga: Abbas Yakubu Yaura
Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, ya yi tir da kakkausar murya kan harin da aka kai wa iyalan Rev. Daniel Umaru na kungiyar EYN da aka fi sani da Cocin Brothers.
Harin dai an kashi a Njairi, Mararraban Mubi da ke karamar hukumar Hong ta jihar Adamawa.
KARANTA WANNAN LABARIN: https://dimokuradiyya.com.ng/tinubu-zai-dawo-najeriya-bayan-ya-ziyarci-kasar-faransa/
Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe ‘ya’yansa maza biyu tare da yin garkuwa da ‘yarsa ‘yar shekara 13, yayin da aka harbe malamin da matarsa wanda har yanzu yake murmurewa daga firgicin da aka aikata.
SGF a cikin wata sanarwa da ofishin yada labaransa ya fitar a ranar Juma’a, ya tabbatar wa ‘ya’yan kungiyar a shirye suke na kare ‘yan kasar daga irin wadannan munanan hare-hare, ya kuma bukaci ‘yan kasar da su bai wa jami’an tsaro hadin kai ta hanyar samar da bayanai kan lokaci domin dakile irin wadannan hare-hare.
Ya kuma yi alkawarin cewa masu aikata irin wadannan munanan laifuka ba za su tafi ba tare da an hukunta su ba.
Ya kuma jajanta wa Rabaran Umaru da iyalansa game da wannan mummunan hali da suka samu, inda ya tabbatar da cewa gwamnati na raba musu radadin da suke ciki a wannan lokaci sannan kuma za a gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban kuliya.
Boss Mustapha ya jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar Adamawa da iyalan marigayi Umaru da ‘yan uwa da addu’ar Allah ya basu ikon jure wannan rashi.
A Wani Labarin Kuma Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya isa garinsa Daura, a jihar Katsina, domin gudanar da babbar sallar, da yammacin ranar Juma’a.
Tun da farko dai shugaban ya isa filin jirgin sama na Umaru Musa Yar’adua dake Katsina, inda daga nan aka dauke shi zuwa tsohon garin a cikin jirgi mai saukar ungulu.
Ya isa Daura ’yan mintuna kadan zuwa 6:00 na yamma ga mai martaba sarki Alhaji Faruq Umar da sauran manyan baki a garin.
Kamar yadda muka samu, Shugaban kasar zai kasance a Daura a duk tsawon lokacin Sallah inda ake sa ran zai bi sahun ‘yan uwansa domin gudanar da bukukuwan Sallah.
Ana kuma sa ran zai yi amfani da hutun Sallah wajen gudanar da al’amura na sirri.