By Abbas Yakubu Yaura
Rahotannin na nuni da cewa A kalla mutane tara ne suka hallaka a wani harin bam da aka kai da wata mota kusa da filin jirgin sama a Aden babban birnin kasar Yemen na wucin gadi.
An bayar da rahoton cewa mutane 12 sun jikkata a harin na ranar Asabar, wanda Fira Minista Mueen Abdulmalek Saeed ya kira harin da ta’addanci.
Shaidun gani da ido sun bayyana cewa daga cikin wadanda suka mutu akwai mata da kananan yara, kuma kawo yanzu babu wata kungiya da ta dauki alhakin kai harin.
Sai dai Kafofin yada labaran cikin gida sun ce harin yazo ne a daidai lokacin da gwamnan Aden ke sauka a filin jirgin, amma bai ji rauni ba.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Makwanni uku da suka gabata an yi yunkurin kai wa gwamnan hari a wani harin bam da aka kai a baya, amma mutane shida sun jikkata a yayin harin.
Harin na ranar Asabar shi ne mafi muni a Aden, baya ga wanda aka yi a watan Disambar bara inda mutane 22 suka mutu.
Comments 1