Jakadar Nijeriya a kasar Burkina Faso, Ramatu Ahmed, ta bayyana cewa akalla ‘yan Nijeriya mata dubu 10 ne aka tursasawa yin karuwanci a Burkina Faso. Ramatu Ahmed ta bayyana hakan ne a yayin ganawarta da manema labarai a birnin Ouagadougou a kasar ta Burkina Faso a ranar Litinin.
Ta tabbatar da cewa mafi yawan wadanda suka fada Harkar karuwancin yara mata kanana ne, wanda suka fada mawuyacin hali a birnin Ouagadougou da kuma wuraren da ake harkokin dibar ma’adanan kasa a yammacin Afrika. Ramatu Ahmed wacce ta kasance a Burkina Faso tun watan Agustan 2017, ta ce daga lokacin an yi nasarar dawo da matan Nijeriya 200 zuwa gida.
Ta kara da cewa; da yawan matan ana musu alkawarin aikin yi ne a kasar da kuma kasashen Turawa daga masu safarar su, sai dai kuma a cewarta ba su san suna dawo wa.