Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya danganta mummunar ambaliya da tasirin sauyin yanayi, yana mai cewa lamarin gaskiya ne.
Abubakar, wanda ya yi magana a gidan gwamnati da ke Yenagoa, a wata ziyarar jaje da ya kai wa gwamnan jihar Bayelsa, Douye Diri, a ranar Talata, ya bayar da gudunmawar kudi naira miliyan 55 ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a jihar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Matsalar Tsaro Mafi Muni Ta Kare Yanzu Nijeriya Ta Samu Lafiya — Lai Mohammed
Abubakar, wanda ya sanar da bayar da gudummawar Naira miliyan 50 a lokacin ga Diri da kuma wata Naira miliyan 5m a sansanin ‘yan gudun hijira na tafkin Oxbow da ke babban birnin jihar, ya ce matakin shi ne ya taimaka wajen dawo da wadanda ambaliyar ta shafa.
Ya ce, “Ziyara ta zuwa Yenagoa ita ce in ji kan wadanda irin wannan barnar da ambaliyar ruwa ta shafa a fadin kasar nan. Canjin yanayi na gaske ne. Abin da ke faruwa a Bayelsa yana da ban takaici. An lalata rayukan mutane da ababen more rayuwa.”
Da yake bayyana bala’in a matsayin abin takaici, Abubakar ya koka da yadda yake tasiri ga rayuwa da tattalin arzikin al’ummar jihar, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da masu kishin al’umma da kungiyoyi da su tallafa wa Bayelsa a wannan mawuyacin lokaci.
Tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayar da shawarar kafa wata gidauniya mai zaman kanta da za ta tallafawa wadanda bala’in ambaliyar ruwa ya rutsa da su da kuma wani asusu na wucin gadi ga manoma domin gyara asarar da suka yi da kuma samar musu da jari don noman na badi.
Ya kuma bukaci Gwamnatin Tarayya da ta gina kayayyakin more rayuwa da ake bukata domin dauke wuce gona da iri.
Ya ce idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa, ya yi alkawarin kammala madatsar ruwa a jihar Adamawa tare da daukar wasu matakan da suka dace don ganin Najeriya ba ta samu irin wannan barnar ba sakamakon ambaliyar ruwa.
Dan takarar na PDP ya kuma bayar da tallafin karatu har zuwa jami’a ga ‘ya’yan marigayi dan wasan kwallon kafa, Ernest Peremobowei, wanda ya nutse bayan ceto wasu mutane biyar da ambaliyar ruwa ta rutsa da su a wani hatsarin jirgin ruwa.
“Mutanen da za su iya tsira daga wannan ambaliyar sun yi asarar rayuwarsu kuma suna bukatar duk wani tallafi da za su iya samu. Ina ta’aziyya gare su.
Abubakar ya kara da cewa, “A nawa bangaren da kuma a madadin iyalaina, ina so in sanar da bayar da kudi naira miliyan 50, sannan ina kira ga abokaina na kamfanoni na duniya da su taimakawa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa.”
Gwamna Diri ya ce mutanen jihar sun samu kwarin gwiwa da nuna soyayya da tsohon mataimakin shugaban kasar ya yi.
Diri, yayin da yake tabbatar da karbar tallafin, ya ce shi ne dan takarar shugaban kasa na farko da ya bayar da irin wannan adadin, yana mai bayar da tabbacin cewa za a biya kudin ne a cikin asusun tallafin da ambaliyar ruwa ta shafa domin amfanin wadanda abin ya shafa.
Sannan ya koka da yadda gwamnatin tarayya ke tafiyar hawainiya duk da kokarin da ta yi na ganin hukumomin da abin ya shafa sun bayar da tallafin daya dace.
Gwamnan Bayelsa ya bayyana Atiku a matsayin uba mai kula da al’ummar jihar tare da nuna kwarin gwiwar cewa zai yi nasara a zaben shugaban kasa na badi tare da hada kai da jihar wajen samar da mafita mai dorewa kan matsalar ambaliyar ruwa.
Ya yi watsi da shawarwarin cewa ruwan sama ne ya haddasa ambaliya, yana mai jaddada cewa ruwan dam na Lagdo da batun sauyin yanayi ne suka haddasa.
A wani labarin kuma, ‘Yan Sanda Sunyi Ram Da Wani Mutum Bisa Zargin Hallaka Mahaifinsa
Rundunar ‘yan sanda a jihar Legas ta kama wani matashi dan shekara 21, wanda ake zargin ya kashe mahaifinsa mai shekaru 70 a duniya.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN, a ranar Talata.