Hukumar kula da Jami’an tsaro na Jahar Ondo “Jami’an Amotekun” ta tabbatar da kama wasu aka zargin suna da hannu a harin ta’addanci da aka ƙaddamar a Cocin St. Francis Katolika ta Owo.
Ƴan Ta’adda dai sun kai hari a Cocin a ranar 5 ga watan Yuni, inda suka kashe kimanin mutane 40, da raunata wasu masu ibada.
KARANTA WANNAN LABARIN: Davido ya bada tallafin karatu ga wani Ɗalibi a Ghana
Kwamandan Hukumar Amotekun Adetunji Adeleye a ranar Alhamis yace sun kama wasu da suke zargin suna da hannu a kisan da aka yi.
Amma bai sanar da mutane nawa suka kama a dalilin harin, amma ya bada tabbacin cewa zasu kama dukkanin waɗanda suke da hannu a harin.
Comments 1