An rantsar da shugaban Gambia Adama Barrow a wa’adi na biyu a ranar Laraba a wasu bukukuwa daban-daban da aka gudanar kusa da babban birnin kasar Banjul, kamar yadda wani dan jarida na AFP ya ruwaito.
Zaben farko na Barrow a shekara ta 2016 ya kawo karshen mulkin kama-karya da aka shafe sama da shekaru 20 ana yi a karamar kasa ta yammacin Afirka karkashin ikon Yahya Jammeh.
An sake zaben Adama Barrow ne a watan Disamba, inda ya lashe kashi 53 na kuri’un da aka kada.
An rantsar da shi wa’adi na biyu na shekaru biyar a wani filin wasa na Bakau da ke wajen birnin Banjul a bikin da ya samu halartar manyan jami’ai na kasashen waje.
An gudanar da zaben na Disamba cikin lumana, kuma shi ne zabe na farko a kasar Birtaniya da ta yi mulkin mallaka na mutane miliyan biyu tun bayan da Jammeh ya yi gudun hijira a watan Janairun 2017 bayan da ya sha kaye a yayin zabe.
Jammeh ya shafe shekaru 22 yana mulkin kasar, inda ya ke jagorantar gwamnatin da ake zargi da cin zarafi al’uma da suka hada da kisa da azabtarwa.
Jam’iyyar United Democratic Party na jagoran ‘yan adawa Ousainou Darboe ya daukaka kara kan sakamakon zaben zuwa kotun koli, yana zargin rashin bin ka’ida da cin hanci da rashawa a yakin neman zaben Barrow. Yayin da kuma Kotun ta yi watsi da rokon.