Dalibai ‘yan aji uku a karamar Sakandare (JSS3) a jihar Kaduna za su koma makaranta a ranar 17 ga watan Agusta, kamar yadda gwamnatin jihar ta sanar a ranar Juma’a a Kaduna.
Sakatariyar ma’aikatar ilimi ta jihar, Phoebe Yayi ita ce ta sanar da ranar komawa a wata sanarwa da ta fitar.
Wakilinmu ya labarto mana cewa Phoebe Yayi ta ce ‘yan JSS 3 din za su koma ne domin rubuta jarabawar ‘BECE’ ta kammala karamar Sakandare wanda za su rubuta a ranar 24 ga watan Agusta.
Ta kara da cewa; ma’aikatar ilimin ta bai wa dukkanin shugabannin makarantar Sakandaren umurnin yin shirye-shiryen domin karbar daliban ‘yan JSS3 a makarantun kwana a ranar 16 ga watan Agusta da kuma daliban makarantar je ka ka dawo a ranar 17 ga watan Agusta din.
“Dukkanin makarantun gwamnati da masu zaman kansu dake jihar, an ba su mako guda daga ranar 16 ga watan Agusta su gudanar da shirye-shiryensu”, inji ta.
Ta ci gaba da cewa; wannan shirye-shiryen yana da alaka da dokokin dakile yaduwar cutar korona da aka sanya, kamar yadda yake ga dalibai ‘yan SSS3.
Ta shawarci masu makarantu masu zaman kansu da su ma su bi dokokin dakile yaduwar cutar. Ta tabbatar da cewa suma jarabawar sauran dalibai ‘yan aji SSS 1, SSS 2 da JSS 1 da JSS 2, da kuma ‘yan firamare za a sanar da ranar komawarsu. Ta kuma tabbatar da cewa ma’aikatar ilimin za ta ci gaba da karantar da daliban ta hanyar Intanet, Rediyo da sauran manhajojin karatu kafin har a koma makaranta na dindindin.
A karshe ta jinjinawa dukkanin masu ruwa da tsaki a bangaren ilimi a jihar, ciki kuwa harda kungiyoyi da kuma kungiyar Malamai da iyaye, da shugabannin makarantu masu zaman kansu, kungiyoyin tsoffin dalibai da kafafen watsa labarai bisa goyon bayan da suke ba su.