Dan takarar jam’iyyar APC, Ismail Danbaba, ya lashe zaben da aka sake na majalisar jiha mai wakiltar mazabar Nasarawa ta tsakiya.
Iiyasu Umar, jami’in hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC shi ne ya bayyana sakamakon zaben da ya gudana a ranar Asabar a Nasarawa.
Da yake bayyana sakamakon, Umar ya ce dan takarar jam’iyyar APC ya samu kuri’a 7,475 inda ya doke Bage Nuhu na jam’iyyar PDP da ya samu kuri’a 4,608.
Ya kara da cewa; a yayin zaben da aka sake, an jefa kuri’a 12,217, a yayin kuri’a 12,083 kawai ce aka kada ta da kyau. Inda kuma kuri’a 134 ta lalace. A don haka jami’in INEC din ya ayyana jam’iyyar APC a matsayin wacce ta lashe zaben da kuri’a masu yawa.
Rahotanni sun bayyana cewa INEC ta sake zaben ne biyo bayan mutuwar dan majalisa mai wakiltar yankin, Alhaji Suleiman Adamu (APC), a ranar 30 ga watan Afrilun 2020.