Wakilinmu Mohammad Gambo Yobe
Gwaman jihar Yobe, Alhaji Mai Mala Buni ya kai ziyarar gani da ido a filin Jirgin da ake ginawa a Damaturu, Babban Birnin Jihar Yobe.
A ziyarar gwamna ya yi hira da “yan jarida, inda ya shaida musu cewa, Gwamnatin shi za ta karasa dukkanin aiyukan da Gwamnatin Ibrahim Gaidam ba ta kammala ba, kuma za su inganta wanda aka yi kamar yadda ya yi alkawari ga Talakawa lokacin yakin neman zaben 2019.
A jawabin Gwamna Mai Mala Buni yayi kira da ‘yan kwangila da su yi amfani da nagartattun kayan aiki masu kwari kamar yadda sukayi yarjejeniya da Gwamnati, kuma yayi kira da su hanzarta wajen kammala aikin su.
Aikin gina filin jirgin yakai mataki na 55% na kammalawa, a yadda Sakataren ma’aikatan Ayyukan jihar Yobe, Malam Abdullahi Jawa, ya bayyana a jawabin sa.