A ranar Alhamis ne jam’iyyar PDP a jihar Benue ta yi barazanar maka hukumar DSS da gwamnan jihar, Rev Fr Hyacinth Alia, a kotu, bisa ci gaba da tsare wasu shugabannin kananan hukumomi hudu.
Sakataren yada labaran jam’iyyar na jihar Bemgba Iortyom ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin da yake bayyana halin da shugabannin kananan hukumomim ke ciki a tsare a hannun hukumar DSS, kamar yadda Tribune Online ta rawaito.
KARANTA WANNAN: Da Dumi-Dumi: An Danka Abba Kyari a Hannun Beli, Bayan Shafe Watanni 18 A Gidan Yari
Iortyom ya lissafo shugabannin da aka kama sun hada da shugabar karamar hukumar Ushongo, Misis Veronica Gajir, shugaban kungiyar kananan hukumomin Najeriya ta jiha wadda ta hada da shugaban karamar hukumar Guma, James Oche da Alfred Atera, shugabannin kananan hukumomin Ado da kuma Katsina-Ala.
Iortyom ya yi kira ga gwamnan jihar, Rev. Fr Hyacinth Alia, da hukumar DSS, da su gaggauta sakin shugabannin kananan hukuumomin hudu da ke hannunsu ko kuma su fuskanci fushin shari’a.
Da yake zantawa da manema labarai a sakatariyar jam’iyyar ta jihar dake Makurdi a ranar Alhamis sakataren yada labaran jam’iyyar ya ce,
“Ya zama wajibi ayi kira ga gwamnan jihar Binuwai, Hyacinth Alia, a kan ci gaba da gudanar da munanan ayyukan da ya yi tun bayan hawansa mulki, wadanda suka hada da kamawa da kuma tsare shugabannin zartarwa na kananan hukumomi hudu na jihar.”
“A ranar Litinin, 3 ga watan Yuli, 2023, shuwagabannin kananan hukumomin Guma, Katsina-Ala, Ushongo, da Ado, sun amsa wata gayyata daga hukumar DSS ta jiha dake Makurdi, bisa umarnin gwamnan, kuma tun daga wannan lokacin da suka gayyace su aka tsare su a can.
Ya kara da cewa, “yau sama da sa’o’i 72 kenan hukumar DSS take ci gaba da tsare shugabannin kananan hukumomin ba tare da bayyana laifin da suka aikata ba, ko kuma gurfanar da su a gaban kotu.
“Hakan yana da kyau a ce laifin nasu zai iya zama kawai kin mika wuya ga rashin bin ka’ida na zargin dakatar da su daga aiki a karkashin umarnin Gwamna Alia.”
Iortyom ya ce da farko a ranar Alhamis, 6 ga watan Yuli, an hana lauyoyi da ma’aikacin kotun majistare da ke neman gudanar da ayyukan kotun a hedkwatar DSS da ke Makurdi domin aiwatar da muhimman hakkokin bil’adama na shugabannin majalisar da ake tsare da su a harabar hukumar, kuma babu wanda ya halarci taron saboda aikin da suka yi a can.
Sakataren yada labaran jam’iyyar ya bukaci hukumar DSS da ta yi hattara da kwararriyar kimarta tare da kawar da muradin Gwamna Alia na aikata rashin adalci da kuma haifar da wani tsari na rashin bin doka da oda a jihar.
JARIDAR DIMOKURADIYYA ta rawaito cewa an zabi shugabannin kananan hukumomin 23 a jihar Benuwe a karkashin jam’iyyar PDP a ranar 30 ga watan Afrilun shekarar 2022 a zaben kananan hukumomin da hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Binuwai (BSIEC) ta gudanar.
Sannan an rantsar da su a ranar 29 ga watan Yunin shekarar 2022, na wa’adin shekaru 2 kamar yadda aka tanada a cikin dokar kafa kananan hukumomi ta jiha wanda wa’adin su zai kare a ranar 28 ga watan Yunin 2024.
A wani labarin kuma, Ma’aikatan Wata Jiha a Arewa Sun Bada Sharadi Kafin Su Dakatar da Yajin Aiki
Ma’aikatan gwamnatin Filato za su dakatar da yajin aikin da suke yi idan gwamnati ta biya su albashin watannin Fabrairu da Maris, kamar yadda shugaban kungiyar NLC, Eugene Manji, ya bayyana a Jos ranar Laraba.
Idan dai za’a iya tunawa a ranar 11 ga watan Mayu ne ma’aikatan jihar Filato suka shiga yajin aikin sai baba-ta-gani bayan gwamnati ta gaza biyan bukatunsu da suka hada da biyan albashi da sauran hakkokinsu.